Saturday 12 November 2016

ADALILIN GATA 6-10

[9:31AM, 11/9/2016] *SDY* *JEGAL*: ���� *ADALILIN GATA*����

                 *(6)*

*DAGA TASKAR Y'AR MUTAN JEGA*

®NWA
*NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*

Kamar kullum yau ma ta gama kimtsa komai na kula da gidan suka shirya suka fito sai mazaunin su na bara, wanda kullum suka fito wani irin mugun nauyi take ji a ranta.

Saboda a tunanin ta kamar ta ya ci ace ta wuce zama y'ar jagora, sai dai ba yanda za tayi sanadiyyar in har bata kula da mahaifinta ba wa ye ta ajiye da zai kula dashi yanda yadace.

Ga shi dai in har ta ce baza su fito yawon bara ba to batasan wa zai ciyar dasu da sauran lalurorin su ba, tunda mahaifinta ba yada idon da zai fita yane mo musu abinda za suyi lalura.

Don ma Malam Inuwa na k'ok'arin basu abincin dare, duk da shi kan shi ba wata wadata ce dashi ba saboda ba kullum za'a ci abinci sau uku a rana gidan shi ba.

Duk ita kad'ai ke wannan tunanin a ranta, wanda har kullum take tunanin ina za ta ne mo masu mafita akan wad'annan matsalolin.

Sanadiyyar bugawar da motocin biyu suka yi ya janyo hankalin tsirarrun mutanen da ke zaune gefen hanya.

Dattijuwar na fitowa daga motor ta ya tayarda hannu zai sharara mata mari.

Hannun da ya ji ya rik'e na shi hannu ne ya bi da kallo.

"Ka daraja mutum ko da baka san shi ba, wanda ya girme ka haka yake tamkar yaya a gurin ka, haka zalika wanda ya yi sa'ar mahaifin ka tamkar mahaifin kane".

"Bai kama ce kaba kuma hakan bai dace dakai ba, yanda ka daraja manyan ka haka Allah zai sa a daraja na ka iyayen ko bayan idon ka".

Cikin sanyin jiki ya bi dattijuwar matar da kallo, sai wata irin kunya ce ke ratsa ga66an jikin shi, hak'uri yafara bawa matar had'e da neman yafiyar abinda ya tashi aikatawa.

Su duka biyun suka bi gurin da kallo domin ganin ta ina za su ga yarinyar amma ina ta 6acewa ganin su.

*********

Sandar mahaifinta ta rika suka doshi hanyar gida. "Zajla ki daina saka kan ki a cikin rayuwar wa'annan mutanen, ba mutunci ne dasu ba".

"Baba ai Ba  komai na yi ba nasiha ce kawai na yimai saboda abinda naga ya kusa aikatawa bai dace ba".

"To Allah yamaki albarka yaba ki miji nagari inga auren ki da jikoki na".

"Baba ni fa na gaya ma bazan yi aure ba, saboda bansan wa zai kula dakai ba", tana maganar ne had'e da zum6uro baki tamkar yana ganin ta.

"Haba Zajla kidaina fad'ar hakan, Allah zai kula dani saboda shi ya so gani na hakan kuma zai ya yemin lokacin da ya so. Tunda abin ciwo ne bana halitta ba kuma daga baya ya same ni".

"Baba kayi ta addu'a Allah yaba ni hanyar samun kud'i insa a gyara ma idon ka".

****

Fitowa tayi da sunan kai ziyara company maigidan ta, amma sanadiyyar abinda yafaru ne ya sa duk ta ji ba za ta iya k'arasawa ba akalar motar ta taja takoma gida.

Da shigar ta falon Saudat tagani zaune tana waya, ganin shigowar Mum ne ya sa ta yi saurin tsinke wayar had'e da mik'ewa tsaye.

"Mum ba dai har kinje company kin dawo ba?".

"Ban k'arasa ba na dawo". Ta ba ta amsa a tak'aice, ganin 6acin rai kwance saman fuskar Mum ya sa bata k'ara magana ba.

"Me ya hana ki zuwa skul yau?".

"Mum fa har na shirya Hafsat takira ni ce wa lecturer d'in bai zo ba shiyasa nayi zama na saboda dama yau shi kad'ai muke da".

Bayan ta bawa y'an aiki umurnin abinda za'a dafa abincin rana, bedroom d'in ta ta wuce duk ranta jagule.

*02:30*
Talatu mai aiki ce ta gayawa Saudat ta fad'awa Mum an kammala komai.

Bedroom d'in ta wuce ta gaya mata sak'on k'are girkin, nan Mum ta bata umurnin kiran Brother su had'u falon Baban su.

Bayan sun kammalu anyi lunch an k'are ne ta kai duban ta ga Al'amein.

"Za ka iya tuna ranar da kashigowa Dad d'inku cikin 6acin rai har kana gaya mai ka mari wani dattijo?".

"Mum me ya kawo wannan maganar?, ai ina ga ta wuce, ko kuma wani fad'an za'a maimaita min?". Yana maganar ne had'e da murmushi a fuskar shi.

"Kaba ni amsa kawai". Ta furta a tak'aice.

"ina ga za'a yi sati biyu ko kwana goma".

"Wannan dai-dai yake da maimaita abinda ka aikata akan fuskar mahaifiyar ka", tana kaiwa k'arshe ta fad'a bedroom d'in Dad.

Cikin razana su duka uku suke kallon junan su kowanne 6acin rai kwance a fuskar shi musamman Al'amein da har jiyojin kanshi sun fara bayyana.

(4 breakfast, luv y'all My fan's)

® *SDY JEGAL*

Dedicated to Anty ```Jidda``` ```Musa```.
[4:08PM, 11/9/2016] *SDY* *JEGAL*: ���� *ADALILIN GATA*����

                   *(7)*

*DAGA TASKAR Y'AR MUTAN JEGA*

®NWA
*NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*

"To wai Dad wa ye ya isa har ya d'aga hannu ya kai wa Mum mari kuma ya zauna lafiya a garin nan?".

"Son ni ma wannan shi ne abinda nake tambaya, amma nasan ba wanda zai bamu wannan amsar sai ita kanta, kuma nasan mu shekara muna tambaya ba za ta gaya mana ba".

"Dad mushiga daga ciki muji ko za ta gaya mana d'an gidan uban waye shi". Ce war Saudat.

Hakan suka d'unguma sai bedroom d'in Dad domin sa mun amsar  tambayoyin su.

"Mum Alamein ta shi kigaya min wane isasshe ne zai d'aga hannu duk garin nan yadakar min Mata?".

Wani guntun murmushi ne ta saki a fuskar ta had'e da girgiza kai alamar ina tausayin tsarin ku.

"Wannan shi zai tabbatar muku ce wa duk abinda kayi na alkhairi ko na sharri za ka had'u da makaman cin shi ko mai dad'ewa".

"Kuma kai da kake ta da jiyojin wuya me za kayi akai ko da na gayama wa ya mare ni? Ko ka manta shi wanda ka mara yana da y'ay'a kuma sun san darajar shi".

"Me kake tunani a wancan lokacin in har ace ko da ka mare shi wani d'an shi na gurin? Ko kana tunanin dukiyar ka za tasa in har suna gurin su k'yale ka?".

"Mum ni fa mutumen laifi ya yimin, har ta ya ya zai zo yana tafiyar ganin dama a saman titi".

"Haka zalika nima laifi nayi yaron ya mare ni".

Cikin damuwa Dad ya bi ta da kallon mamaki, ya rasa ga ne ita wace irin Mace ce da batasan y'ancin kanta ba.
 
Durk'usawa ya yi gabanta ya d'ora hannuwan shi saman k'afafun ta tamkar yayi kuka yake ji ya furta.

"Don Allah Mum ki gayamin ya akayi hakan ta faru? Kuma in kin san waye ki gayamin shi please and please Mum?".

Murmushi ta yi sosai har hak'oran ta suka bayyana, sannan ta kwashe ko mai ta gaya masu had'e da yaba halayyar yarinyar.

Sai lokacin suka saki fuskokin su har Al'amein na furta "wallahi ya kuru da ya aikata wannan d'anyen aikin da ya had'u dani".

"Inna san waye shi ko in ban sani ba? Ko kuma inna gaya maku waye shi za ku d'auki mataki?".

Da hakan dai ta k'ara janyo hankalin su had'e da k'ara lurar dasu kan muhimmancin girmama na gaba dasu, wanda Dad ke zaune yana sauraren su.

******

Duk abinda aka saka ma rana zai zo indai da rai da lafiya. Yau ne ake shirin gabatar da musabak'a ta gari wadda za'a gabatar a makarantar su Zajlah saboda kasancewar makarantar ta su ce babba kuma itace kan gaba a duk sauran makarantin nen garin su.

Daga kan y'an izifi biyu aka fara har zuwa kan izifi sittin wanda aka share sati d'aya ana gudanarwa tsakanin makarantu biyar dake garin.

Inda aka k'are kuma makarantar su Zajlah ta zamo gwarzuwa a musabak'ar wanda har da Zajlah da Salmat acikin gwarzayen, saboda Zajlah ta yi haddar izifi talatin inda Salmat ta yi izifi ashirin.

Bayan kwana ki bakwai ne aka gabatar da ta Jaha a garin Birnin kebbi, daga nan akayi ta k'asa gaba d'aya inda Zajlah ta zo ta d'aya a cikin y'an izifi talatin Salmat kuma ta biyu a cikin y'an izifi ashirin.

Sun sa mu kyaututtuka da dama wanda ya had'a da kud'i da keken d'unki Zajlah harda kujerar Makkah wanda sanadiyyar hakan har da guntun hawayen ta na farin ciki.

Ko Malaman su kaduba lokacin za kaga farin ciki kwance fal a fuskokin su musamman Ustaz Lukman dake kula da 6angaren masu haddar da kuma wani abu da yake ji kwance k'asan zuciyar shi akan Zajlah.

Mahaifin ta farin ciki fal a ran shi harda hawayen shi, ji yake yi ina ma ace yana gani da idon shi yaga wannan rana ta farin ciki da y'ar shi ta zamo gwarzuwar shekara.

Hakan suka tarkata suka dawo gida farin ciki fal ransu, sai mak'ota ke ta shigo masu murna da Allah sanya alkhairi.

Sun samu kud'i sosai musamman Zajlah da tazo ta d'aya, har gida Ustaz Lukman ya biyo su had'e da kyaututtukan da suka sa mu mota ta kawo masu har k'ofar gida.

"Za ku sa mu shigowa makaranta ranar assabar?", ce war Ustaz Lukman.

"Ustaz a bamu sati d'aya mana mud'an huta sannan mu shigo".

"Sati d'aya ya yi yawa gaskiya saboda bazan jure...... Sai kuma ya canja akalar maganar.

"Shikenan Zajlah ku shigo zuwa ranar Larba, tunda kunga yau ta kama Assabar".

"To Ustaz mun gode sosai". Da hakan suka shige gidan su Salmat d'in.

® *SDY JEGAL*

Dedicated to Anty ```Jidda``` ```Musa```.
[10:33AM, 11/10/2016] *SDY* *JEGAL*: ���� *ADALILIN GATA*����

                  *(8)*

*DAGA TASKAR Y'AR MUTAN JEGA*

®NWA
*NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*

Kamin su shiga gidan ne Salmat ta kai duban ta zuwa ga Zajlah had'e da furta.

"Yau kin yarda da abinda nake cewa Ustaz Lukman son ki yake yi?".

"Ke dai ina ga aure kike so shiyasa kullum maganar ki ba ta wuce ta So ba".

"Kina ji fa yau har da furta cewa bazai juri rashin ganin ki ba, sai ya juya maganar saboda kar mu gane inda ya dosa".

Dundu ta sakar mata had'e da janyo gashin kanta sai da ta yi k'ara, da hakan suka shiga gidan.

Mama Inno ce ta tarye su dukan su ta rungume sai albarka take saka masu har da guntun hawayen ta.

"Zajlah yau burin ki zai cika da yardar ubangiji saboda ya yi maki hanyar samun kud'in da za ki kula da matsalar idon mahaifin ki".

"Wallahi Mama ina jin tsabar kud'in da nasamu tun a can matsalar Baba ce nafara kawo wa, sai kuma samun abin Sana'a da zai raba mu da yawon bara".

"Don ko babu kud'in zan soke matsalar bara tunda na samu keken d'unki zan tashi da koyo har in iya".

"Gaskiya kam kinyi tunani mai zurfi, yanzu sai abubuwa sunyi sauk'i ku had'u ke da Salmat kuje koyon d'inki".

Da hakan aka shigo da kayan da suka samu gidan su Salmat, inda kowannen su ke da keken d'inkin sai Salmat dake da kud'i dubu d'ari biyu Zajlah ko na da dubu d'ari biyar da kujerar Makkah da shugaban k'asa ya baiwa duk wanda ya yi na d'aya a matakin haddar su tun daga izifi biyu har zuwa izifi sittin.

****

Tun lokacin da yarinyar ta hana ma saurayin marin ta take kwana kuma ta tashi da ita aranta, saboda yarinyar ta burge ta sosai, sai tunani take yi ina ma ace y'ar tace ke da halayyar wannan yarinyar.

Hakan take gurin Fadeel wanda duk yanda ya so yafige yarinyar a cikin zuciyar shi abin ya faskara.

Duk inda zuciyoyin mutum biyu suke da tunanin ta suke kwana kuma suke tashi, duk inda suke farautar ta domin su ganta abu ya faskara.

*******

Falon ta shigo ta d'auki remote domin canja tashar, abinda ta ga an nuno ya hana mata canjawa sai gata zaune jagwaf saman kujera.

"Saudat! Saudat!! Saudat!!!".

Gigice ta fito daga d'akin ta ta fad'o falon saboda kiran da Mum ke ta k'wala mata.

Plasma d'in ta bi da kallo saboda itace Mum ke nunawa da yatsan ta, ita dai bata ga komai ba bayan yarinya tana rero karatun Qur'an cikin baiwa kowane harafi hakk'in sa had'e da tajweed.

"Mum me ke faruwa halan? Ban fahimci me kike nuna min ba fa".

Nan Mum ta yi mata bayanin yarinyar. Hakan itama Saudat ta ji yarinyar ta burge ta sosai.

"Ina so kishirya zuwa anjima ki rakani makarantar su yarinyar nan, dama na yita neman ta duk inda nake sa ran ganin ta bangan taba".

"Yanzu Mum me za kije kiyi mata? Sai kita neman yarinya tamkar wacce ta k'ulla maki wani abin arzik'i".

Mugun kallon da Mum ta bita dashi ne ya sa taja bakinta ta tsuke.

*05:00pm*
Dai-dai wannan lokacin Mum ta faka motar ta k'ofar makarantar, da Ustaz Yusuf ta fara cin karo k'ofar makarantar.

Nan ta yimai bayanin abinda ke tafe da ita, mashin d'inshi yahau yayi mata jagora har k'ofar gidan su Salmat, godiya ta yita yimai har da fitarda kud'i taba shi saidai bai kar6a ba yajuya yakoma.

Mota ta hakimce tana wani yatsinar fuska saboda k'ofar gidan da taga sun tsaya wai nan Mum tazo kuma gurin k'aramar yarinya.

"Fito mushiga ciki mana".

"Shiga ki fito Mum zan jira ki a mota".

Fad'a ta dinga yi mata sannan ta fito har da wani handkerchief tana toshe hanci. Gidan suka shiga inda Mama Inno ta yi masu tarbar da ta dace duk da batasan su waye ba.

Bayan sun gaisa Mum ke yi mata bayanin gurin Zajlah tazo. Nan Mama ta kira su daga d'aki suka fito.

Durk'usawa sukayi har k'asa suka gayar da Mum, bayan ta amsa ne take ta yabon musabak'ar su data gani ana ta haskowa a cikin kowace tasha.

Nan ta d'ora da gaya mata itace ta hana wani saurayi ya mara. Har ga Allah ta manta da abinda ya faru sai yanzu data tuna mata.

"Laaah Haj wallahi ba komai, ai yiwa kaine don ni ma zanso a daraja nawa iyayen".

Da hakan Mum ta basu dubu goma-goma suna ta godiya, itako ta fice daga gidan.

® *SDY JEGAL*

Dedicated to Anty ```Jidda``` ```Musa```.
[6:14PM, 11/10/2016] *SDY* *JEGAL*: ���� *ADALILIN GATA*����

                 *(9)*

*DAGA TASKAR Y'AR MUTAN JEGA*

®NWA
*NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*

Da sannu Fadeel ya binciko gidan su Zajlah wanda karo uku kenan yana zuwa k'ofar gidan su amma sai jikin shi yayi sanyi yaka sa tunkarar ta yakoma.

Yau dai da k'arfin gwiywar shi ya tashi na tunkarar ta yaga ya mata gaskiyar lamari ce wa yana son ta.

K'ofar gidan ya zo, amma a tunanin shi na zai iya tunkarar ta yau sai gashi abin ya gagara, ta gaban shi suka zo suka wuce ita da Salmat domin zuwa koyon d'inkin su gidan wata mata dake k'arshen layin su.

"Ni fa Zajlah abin nan ya fara d'aure min kai, in har kin lura kusan kwana uku kenan duk muka wuce zanga wannan motar".

"Kuma fa abin mamaki ba a ganin na cikin motar su waye saboda duhun glass d'in motar".

"Ke kika damu da wannan motar, ni fa zan iya ce maki ban ma ta6a lura da motar ba sai yau dakika yi maganar".

"Ai ke dama ba komai kike lura dashi ba, inaganin wataran sai halaka ta hau kan ki bakisan za ta zo ba".

"Au dama in abu zai same ka zaka san da zuwan shine?".

"Ba hakan nake nufi ba, amma dai ana so ka lura da yanda abubuwa ke tafiya saboda tsaro".

Dariya sosai Zajlah ta yi, da hakan suka isa gidan da suke koyon d'inki.

******

Yau ne aka aje kan za'a yiwa Baban Zajlah aiki a idon shi, Malam Inuwa, Zajlah da Salmat ne suka yi mai rakiya zuwa Birnin kebbi. Asibitin Sir Yahaya ce aka yi mai aiki kuma aka gama cikin nasara wanda sai da suka had'a shi da medical glass saboda rashin ganin abinda ke nesa dashi.

Je kaga murna fal a gurin Mal Abubakar inda yake alfahari da y'ar shi k'waya d'aya tak da Allah ya bashi, wacce ta zame mai y'a d'aya tamkar da dubu.

*****

*Wacece Zajlah?*

Mal Abubukar d'an asalin k'auyen giwa tazo ne shi da matar shi Basira, auren zumunci ne aka yi masu  domin mahaifiyar ta da mahaifin shi ne uwa d'aya uba d'aya.

Sun ta so tare da Mal inuwa ne tun shigowar shi garin Jega sanadiyyar Sana'ar kayan gwari wanda daga baya har ya samu matsakaicin gida ya saye a kusa dashi ya dawo nan da zama.

Allah ya had'a kan matan su wanda inka gansu zaka rantse da Allah y'an uwan juna ne. Basira ta rasu ne tun ranar da ta haifi Zajlah wanda bata ko saka yarinyar a idon ta ba.

Lokacin ita kuma Mama Inno ta haifi Salmat da sati biyu, nan ta kar6i Zajlah ta had'a da Salmat tana shayar dasu.
      (Asalin sunan Zajlatu ne k'awaye ne suka tak'aita shi da Zajlah, abinda sunan ke nufi rayuwa kyakkyawa kuma mai sunan tana daga cikin tabi'ai, me neman k'arin bayani akan asalin sunan da tarihin mai sunan zai iya searching da *KISASUT TABI'AT*, amma da larabci).

Sun shiga tashin hankali sosai musamman Mama Inno da Mal Abubakar, dole suka dangana saboda wanda yafi su son ta ya kar6i abarsa.

Zajlah na da shekara takwas a duniya  Baban ta ya makance sanadiyyar ya jima yana gani bishi-bishi sai bai d'aukin abin wata matsala ba har abin ya ta6a idon duka ya daina gani, tun yana iya lalurar kan shi har abin ya gagare shi.

Lokacin ne sauran tsirarrin dangin shi suka guje shi sanadiyyar ganin ya zama wata lalura a gare su, wanda shi ba hakan yazauna dasu ba don mutum ne mai taimakon dangin shi duk da shi ma ba wani hali ne dashi ba.

Sanadiyyar makarantar shi ne Zajlah ta dawo gurin shi da zama domin taimaka mai da wasu abubuwan da ba za'a rasa ba.

Zajlah yarinya ce mai kimanin shekara goma sha shida zuwa sha bakwai, chocolate colour ce ba wata kyakkyawa ce ta azo a gani ba sai dai manyan idon ta da gashin girar ta shike fitar da kyawon ta, yarinya ce mai shape  sai dai batada k'iba irin sosai d'in nan.

Kamin abubuwa suyi tsanani ansaka su makarantar boko iya primary daga nan basu cigaba ba sai makarantar Arabic dasuka mayar da hankali akan ta.

Saboda kowaccen su ta yi sauka uku sai kuma hadda da suke yi har Ustaz Lukman ya saka su acikin musabak'a, wanda sanadiyyar ne har duniya tasan da zaman su inda iyayen su ke alfahari dasu.

® *SDY JEGAL*

Dedicated to Anty ```Jidda``` ```Musa```.
[9:08PM, 11/10/2016] *SDY* *JEGAL*: ���� *ADALILIN GATA*����

                  *(10)*

*DAGA TASKAR Y'AR MUTAN JEGA*

www.sadijegal.blogspot.com

®NWA

*NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*

Mamaki fal a ran Saudat na miye silar zuwan Mum gidan su wannan kucakar yarinyar, ga shi tana so ta tambaye ta sai dai kuma bata ga fuskar tambayar ba.

Bayan sun dawo ne direct bedroom d'in Dad ta wuce, zaune yake k'asa saman carpet ya jingina jikin shi da kujera yana karatun jarida.

"Daddyn Alamein hutawa kawai ake yi"?.

"Ba dole ba tunda yanzu kin rage So na da tattali na, ina ga aure zan zo in yi ko zan samu mai bani kulawa", yana maganar ne d'auke da murmushi a dattijuwar fuskar sa.

Murmushi Mum ta yi sosai had'e da tattara hankalin ta guri d'aya ta k'ara matsawa gab dashi.

"Shikenan fad'uwa tazo dai-dai da zama, ka ga inka nemo mata sai a had'a da naka auren dana son ad'aura rana guda".

"Yaushe Son ya nemi mata banda labari? Yaron da ko mata bai cika kulawa ba ina yaga macen da yake so?".

"Sanin hakan ne ya sa na nemo mai mata da kaina, yarinya y'ar asali y'ar gidan mutunci mai ilmi".

Wata irin zabura ya yi ya kai duban shi zuwa gare ta.
    "Kina nufin Son ne za ki yiwa auren dole? Ko ni da nake uban shi ba'a yimin auren dole ba barrantana shi da yake cikin k'urciyar shi", yana maganar ne cikin fad'a-fad'a.

"Dad'i na dakai duk yanda ake magana cikin kwanciyar hankali indai aka ta6o yaran ka cikin second d'aya za ka birkice".

"Duk duniya ba ni da farin cikin da ya wuce na yara na, babu takura ko matsi tsakanina dasu duk abinda suke so shi nake so saboda haka babu maganar ki za6ama son abokiyar rayuwa sai ranar da yaganta da kanshi yakawo ta".

Suna cikin maganar ne sai ga Alamein da Saudat sun shigo d'akin, bayan sun gaida mahaifan sune suka nemi guri suka zauna.

Sai da ta tattara hankalin ta a gare shi sannan ta fara magana cikin hikima da basira.

"Alamein matsayi na na mahaifiyar ka data shayarda kai kuma ta raine ka da gudun 6acin ranka in na nemi wata alfarma gurin ka za ka iya yimin ita?".

"Haba Mum miye duniya bazan iya yi maki ba? Duk duniya banda tamkar ku ke da Dad sai kuma Lil".

"Da kyau Son! Mata na nema ma mai hankali da nutsuwa ga ilmi wanda nake fatar inka amince aure nan da wata d'aya indai har iyayen yarinyar basu yi mata miji ba".

Yanda kasan ana kid'a ganguma haka zuciyar Alamein ke bugawa, cikin abinda bai wuce second biyar ba zufa ta wanke mai fuska duk da sanyin A.c da fanka da suka yalwata d'akin.

"Aure kuma? Mace? Ni da kaina? Bazai yuyu ba, miye abin so ga Mace d'in? Me zan yi da ita? Tauyewar rayuwa kawai".
   "Anya zan iya bijirewa buk'atar Mum? Duk k'ask'anci na nasan darajar mahaifa na, in na yi mata hakan banyi biyayya ba", duk a cikin zuciyar shi yake wannan tunanin.

Ka aure ta kawai in ya so daga baya ka mak'ala mata wani sharrin ka sake ta kawai.

"Bazan so in zamo mai rayuwar auri saki ba shiyasa tun farko Mace ba ta gabana".

Duk a zuciyar shi yake ta sak'a wad'annan maganganun da ya rasa samun mafita akai.

"Mum ina fatar ba wannan maganar ce silar zuwan mu gidan su wannan kucakar yarinyar ba? Me Brother zai yi da wannan mitsitsiyar yarinya, kuma ma y'ar talakawa haba Mum".

Maganar Saudat ta dawo dashi hayyacin shi daga tunanin da ya cunkushe mai zuciya.

"Y'ar talakawa fa? Duk yanda naci buri akan auren Son da bak'i daga k'asashen waje a hakan zan tozarta?".

"Alamein".

Kai ya d'ago ya kai duban shi zuwa ga Mum had'e da saka handkerchief yana sharce zufan da ke karyo mai ga jiki ta ko ina.

"Amsar ka nake jira in har ka amince shikenan, in ma baka amince ba ka gayamin bazan tilasta kaba, sai dai ina hango alkhairi tattare a zaman takewar ku".

"Mum na amince". Da hakan ya mik'e ya fita daga d'akin zuciyar shi tamkar ta fashe.

"Alhamdulillah! Allah na gode ma, yanzu sai ayi haramar zuwa neman aure".

"Ke kuma fitsararriya da kike maganar y'ar talakawa ce na gaishe ki y'ar k'aruna, a hakan dai ta fiki mutunta mutane, ta shi ki 6ace min dagani".

Cikin 6acin rai Saudat ta mik'e sai da ta kai k'ofar fita ta furta "Allah yasa anmata miji kuma har an saka rana", sannan ta fice da sauri.

Murmushi Dad ya yi had'e da ce wa "wannan auren kan ki za ki d'aurawa shi saboda babu mai son shi".

"Saboda son kai da rashin hango abinda nake hangawa ba, amma nan gaba za ku gane inda na dosa.

® *SDY JEGAL*

Dedicated to Anty ```Jidda``` ```Musa```.

ADALILIN GATA 1-5

[8:24PM, 11/4/2016] *SDY* *JEGAL*: ���� *ADALILIN GATA*����

         *(1)*

*DAGA TASKAR Y'AR MUTAN JEGA*

®NWA
*NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*

*GODIYA*
Ina godiya ga Allah mai kowa da komai, mahaliccin sammai da k'assai, mai kashewa mai rayawa, mai badawa a duk lokacin da yaso, maji6incin bawan shi.

Godiya ta tabbata a gare shi daya bani ikon rubuta wannan littafin, kuskuren da ke ciki Allah ya yafemin.

*JIN JINA CE A GARE KU*
Anty Ybk
Benaxir Omar
Umma ta Lubiee Mai tafseer
Bebeelo
Hauwa Jabo
Ummu Abdul
Feenat Ja'afar
Mmn Shakur
Mum Faty
Zarah B~B
Mamu
Autar Haj.

*KUNA RAINA*
Anty Innah
Anty Fatima
Anty Rukayya
Sis Atiks
Sis Maryam Mela.

*BAN MANTA KUBA*
Jegal families
3stars
Hindatu Jegal
Nafeesa Jegal
Aisha Jegal

5stars
Assy Jegal
Sumee Jegal
Balkisu Jegal
Hauwa Jega
Asmee Jegal

*K'ANNE NA NA KAINA*
Yaha Saddik
Bizzy
Yagani
Ummy
Salma
Yasmeeny
Salmatun Innah
Habiba Yayaji
Maryam Idris katsina
Zainab Abdullahi
Naanah
Umamat
Mmn Sajjad
Khairat
Ummeen Alamein.

*K'AWAYEN ARZIKI*
Hindatu shehu
Shema'u Bello Bari
Shafaatu zakariyya
Y'ar gidan Ango
Khadija Manga
Fati Salihu
Balkisu Bilyamin
Jidda A.K.A
Mum Zee
Mmn Jamila
Mmn Hanan
Princess Meenat
Hauwa'u Ag
Mmn Haneef
Mrs Jawaheer
Deeja Abdul
Mrs Zannah
Maryama
Namcy Sadururah
Stylish
Fatima.
Ban manta da sauran ba ku saurare ni a last page.

*YARA MANYAN GOBE*
Halima
Maryam
Khadija
Abduljalal.
Allah yaraya min ku akan sunnah.
Sai yayyen ku
Lawiza & Zainab.

*GORO NE*
Ga dukkan masoya na way'anda na sani da way'anda bansani ba da sannu za ku shigo list d'ina luv y'all.

*SOYAYYAR KU TA DABAN CE*
Nagarta writers association luv y'all, Allah yakara had'a kawunan mu.

*GAISUWA*
Ga kowace Mumcy na.

*SADAUKARWAR TAKI CE*
Anty na, Mai bani shawara had'e da kulawa *Jidda Musa Mmn twin's*.

*TSAKANINA DAKE SAI ALLAH*
Sanah Isma'il Suleiman Matazu.

*LITTATAFAN MARUBUCIYAR*
*FATEEMA*
*BAHIJJA*
*SANADIN K'UNCI*
*ADALILIN GATA*

Cikin shirin shi na alfarma ya fito falon ya durk'usa har k'asa yana gaida mahaifiyar shi. Kafad'ar shi ta rik'o ta mik'ar dashi ya zauna gab da ita.

"Sai ina yanzu son?".

"Mum zanje company ne saboda muna da meeting da za muyi da wasu bak'i ne".

"Sai ka shiga ku gaisa da Dad d'in ka duk da ina tunanin kamar barci yake yi".

"In hakan ne bara kawai in wuce don nasan Dad sai mu wuce 15mnt muna gaisawa, ga shi sauri nake yi".

"Kenan kasan halin abinka nan 6angaren, amma d'ayan 6angaren duk yanda nake lurar da kai ba ka gane wa".

Da saurin shi ya mik'e cikin murmushi ya doshi hanyar fita "inna dawo ma yi maganar".

"Kullum hakan kake ce wa, fatana d'aya Allah yaganar daku baki d'aya".

Yana gab da fita ya ji muryar ta tana furta "Brother ni ma ba za'a tsaya mu gaisa ba kenan"?.

Cikin saurin ta ta k'araso gab dashi, hugging d'in shi ta yi "Mrng Brother".
"Mrng Little Sister, inna dawo za muyi magana".

Da sauri ya fice saboda agogon hannun shi daya duba ya ga saura minti biyar, a k'a idar shi bai son African time yayi ko ayi mai.

Sai da ya hau kan titin ya k'ara gudu sosai saboda saurin da yake yi.

K'eeeeeee kake ji sanadiyyar mugun birkin da yaja wanda saura k'iris ya kad'e mutumen.

Cikin isa da k'asaita da kuma 6acin rai kwance a saman fuskar shi ya fito daga motar.

Mari biyu k'warara ya yiwa dattijuwar fuskar mutumen wanda baki sake ya bishi da kallo.

Hannun shi na dama ya saka ya cire glass d'in shi no respect, yasa d'ayan hannun ya fitar da handkerchief a gaban rigar shi ya goge fuskar shi.

Cikin azama ya koma cikin motar ya tada ta, ganin ce wa zai iya bi saman kan shi yawuce yasa cikin sauri yaja jikin shi gefen titi da mamaki fal a ran shi.

"Ohhh! duniya ho yanzu wannan yaron zai fito ya faffallamin mari hankalin shi kwance kuma yana k'ok'arin takani ya wuce, duniya ce ta ishi kowa riga da wando".

****

Yau kam tana ganin sun makara ga yanda suke fitowa mazaunin su na masu bara gefen wata ma'aikata.
   Bayan sun iso gurin ne ta gayar da wa'anda ta tarar sannan suka ne mi guri suka zauna.

"Har ga Allah ba na son wannan zaman barar da muke yi, kawai abin ne ya riga yafi k'arfi na, don in mun daina bansan miye mafita a garemu ba".

Matar kusa da ita ne ta ta6o ta sanadiyyar wani da ya zo yana raba masu d'ari-d'ari wanda har ya zo kanta bata sani ba nan ta kar6a ta yi godiya.

*12:00pm* suka fara watsewa da kad'an-kad'an inda ita ma Zajla ta rik'a sandar mahaifin ta suka doshi hanyar gida. Asaman hanyar ne suka had'u da yaran da ke tallar zogale da 6ula had'e da k'uli mai magi da yaji.

"Baba ko mu siyi zogale da 6ula?".

"Nawa ne muka sa mu yau hala?". Kud'in ta fitar ta irga taga 350 ne, nan take gaya mai ko nawa ne.

"Siya mana 6ula na 100, zogale da k'uli na 50".

Hakan ta tsayar da yaran ta siya suka wuce gida. Da shigar su gidan ne ta yi masu kwad'o suka ci.

Bayan sun gama ne ta ebi ruwa ta je ta yi wanka ta yi shirin islamiya.

Wasu kod'add'un uniform kalar blue ta saka sannan ta yiwa Baban ta jagora ta fito dashi k'ofar gida cikin inwar icen mangoro gurin su Malam Inuwa.

"Y'ar Baba za'a je makarantar kenan?".

Ta bashi amsa ta re da durk'usa wa ta gaida su. "Sai ki biya ki kira Salmat in ta shirya ku wuce".

Gidan Malam inuwa ta dosa a k'ofar gida suka ci karo da Salmat, hakan suka sa kai sai makarantar su.

(Na so wannan littafin bazan yi posting ba sai 18/11/2016, amma hakan bai samu ba sanadiyyar maganganun wasu da suke furta cewa Jan rai ne. To kuyi hak'uri ba hakan bane daga yau za ku rik'a jina kullum insha Allah, nagode sosai luv y'all)

® *SDY JEGAL*

Dedicated to Anty ```Jidda``` ```Musa```.
[7:07AM, 11/5/2016] *SDY* *JEGAL*: ���� *ADALILIN GATA*����

                *(2)*

*DAGA TASKAR Y'AR MUTAN JEGA*

®NWA
*NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*

Suna shiga islamiyar suka tarar da mutane na alwala sanadiyyar kiraye-kirayen sallar azahar da ake yi ko ina, nan su ma suka yo alwala suka bi jam'i akayi sallah.

Bayan sun k'are ne suka wuce ajin su na d'aukar hadda, hakan suka biya da d'ai d'aya inda Ustaz Lukman ke sauraren su had'e da gyara ga duk wanda ya yi kuskure.

Da hakan suka k'are har la'asar ta yi suka fito akayi sallah.
    A k'a idar makarantar duk ranar larba za'a za 6i d'alibai uku cikin Maza uku cikin Mata domin gabatarda abubuwan da ake koya masu a cikin class.

Hakan ta kasance yau ga d'aliban da aka za6a sun fito sun gabatar da abubuwan gwanin sha'awa ga ma su saurare.

K'arfe shida na yamma aka tashi kowa ya ka ma hanyar zuwa gida. Asaman hanyar ne Salmat da Zajla suke tattaunawa.

"Gaskiya Salmat yau sai gaba na ke fad'uwa na zata Ustaz Lukman zai sanya ni a cikin masu karatun satin nan".

"Tabbb! Ai kima shirya kinsan satin sama dole za ki shigo a cikin wa'anda za su yi".

"Ni fa abinda naso su bar mu muji da karatun haddar mu tunda lokacin musabak'a na k'aratowa".

"Lallai ma Zajla kin kai, kawai kije kiyi ta bitar haddar ki sannan ki zauna da shirin fitowa larbar sama karatu gaban ko wa".

"Muguwa kawai tunda kin ga kin yi yau hankalin ki ya kwanta ai zaki rik'a kayar min da gaba", tana maganar had'e da kai mata dundu a bayan ta.

"Gaskiya kar ki tayar da hankalin ki abin baida wata fargaba kawai dakin fito dakewa za kiyi, kuma kar ki rik'a kallon mutane ki nok'e kan ki kawai".

"Shikenan Allah yakai muna rai yasa fargaba ta fice min kamin ranar".

"Ameen", ta amsa a gajarce.

Da hakan har suka k'araso gida, a tare suka shige gidan su Salmat d'in saboda wannan k'a idar ta ce in sun da wo daga islamiya gidan su Salmat take zama har sai Baban ta sun k'are hira sannan ta fito su shiga gida.

****

Cikin 6acin rai ya shiga d'akin meeting d'in wanda sanadiyyar hakan kowa ya sha jinin jikin sa.

Hakan akayi meeting d'in rayuwar sa 6ace wanda mataimakin shi ne Imran ya jagoranci komai har aka k'are.

Bayan bak'in sun wuce ne wani cikin ma'aikatan ke ba da shawara kan ce wa me zai hana ayi musaya da wa'ancan bak'in a basu fata suko su bada ire-iren takalma, jakunkuna da sauran dangin kayan da ake sarrafawa da fata d'in?.

Ya cigaba da ce wa "a tunani na hakan zai fi akan abada fatar su bada kud'i ko ya kuke gani?".
   Ya k'arashe maganar had'e da kallon mutane cikin nu na bajin ta kan shawarar da ya bayar.

Kallon da mutane suka bishi da shi ne na alamar ba kada hankali, wasu kuma na tausayawa gare shi ya sa ya sha jinin jikin shi ya yi tsit.

Ko wa ya yi zugum domin jiran me zai biyo bayan maganar da ya furta, saboda duk yanda aka zauna meeting ba bu mahaluk'in da ya isa yace tak ba tare da ya bashi dama ba, barrantana yau da ya shigo rai 6ace wanda ya hana yayi magana har akayi meeting d'in aka k'are.

"Duk da ce wa kai bak'o ne a wannan ma'aikatar bazai hana hukunci na yahau kanka ba".

Cikin damuwa Imran ya tari numfashin shi had'e da bashi hak'uri amma ina ya gama furta "na sallame ka daga yau".

Hakan ya ta shi tamkar guguwa yabar gurin cikin mintunan da basu wuce uku ba.

Durk'ushe ya yi gaban mataimakin A.K.A kuma babban aminin shi yana mai bada hak'uri had'e da furta

"In har kuka sallame ni bansan ina zan dosa ba, da wannan aikin nake kula da mahaifiya ta da sauran k'anne na marayu".

"Sai dai kayi hak'uri aikin gama ya gama duk nan ba wanda ya isa ya janye wannan hukuncin".

"An samu matsala ne tun farko ba'a gaya ma tsarin shi ba shiyasa, ko ni nan da nake mataimakin shi kuma babban aminin shi indai a office ne ban isa yayi magana inyi ba har sai ya bani dama".

Hakan sauran ma'aikatan suka rik'a bashi hak'uri had'e da fatan alkhairi saboda bakin alk'alami ya bushe, don shine mutum na bakwai da hakan ta kasance dashi tun lokacin da mahaifin shi ya yi ritaya ya bashi kula da company d'in, da hakan kowa ya Kama gaban shi.

Mutum biyu ne suke tattaunawa akan matsalolin da ke faruwa a ma'aikatar.

"Gaskiya wannan ma'aikatar ba ta nesa da rushewa, kaduba kaga yanda yaron nan ke shuka rashin mutunci son ranshi", cewar tsamurarren.

"Tabb to ai abin gado ne haka mahaifinshi yake tsula tsiya lokacin da yana manager, don ni na rasa gane tsakanin d'an da uban wa yafi rashin mutunci", a cewar bak'in mutumen kakkaura.

"To Allah yayi masu magani, kuma yaganar dasu".

"Ameen".

® *SDY JEGAL*

Www.sadijegal.blogspot.com

Dedicated to Anty ```Jidda``` ```Musa```.
[5:16PM, 11/6/2016] *SDY* *JEGAL*: ���� *ADALILIN GATA*����

                  *(3)*

*DAGA TASKAR Y'AR MUTAN JEGA*

www.sadijegal.blogspot.com

®NWA
*NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*

Hakan ya fad'o gidan ko sallama babu sanadiyyar wani huci da yake yi shi ala dole an 6ata mai rai fuska tur6une tamkar namijin zaki.

Da saurin shi ya ta shi ya taryo shi yana bubbuga bayan shi, sanadiyyar ya k'i jinin jure damuwar d'an shi komi k'ank'antar ta.

"Wa ya ta6a uba ga Dad kuma d'a ga Dad?, bazan juri ganin ka cikin 6acin rai ba komai k'ank'antar shi".

Ruwa ya tsiyaya a cup ya d'ora mashi a baki ya kauda kai yana huci, d'ayan gefen ya mayar da cup d'in sannan ya sha kad'an ya kauda kai tamkar wani jinjiri.

"Gayamin Babana meke faruwa, kuma wa ya 6ata ma rai?".
    Mum baki ta sake tana kallon sarautar ubangiji, abu gwanin haushi.

Cikin yanga tamkar wata mace ya kora mai abinda ke faruwa.

"Yo banda abinka Son miye laifin wanda ya baka shawara akan cigaban ka?, kuma wai har za ka iya ta da hannu ka fallawa dattijon mutane mari", Mum ce ke wannan maganar cikin 6acin rai da fad'a-fad'a.

"To shi dattijon titin uban sa ne da zai zo yana tafiyar yanga akai?", cewar Dad.

"Wallahi dai ku bi duniya a sannu daga kai har yaron ka, shin kud'i hauka ne? Su talakawan su sukaso ganin Kansu a hakan? Ku da kuke hakan siya kukayi aka baku gyara?, bai dace ka rik'a nunawa yaran nan gatan da yazarce misali ba".

"Mu shiga daga ciki Son, saboda ta fara wa'azin nan na ta da take zama alarammar kan ta taja kuma ta fassara", hannun shi ya rik'a suka haura sama sai bedroom d'in shi.

"Mum wannan abin fa ya kusa yawa, miye laifin wanda zai kawo cigaba akan lamurran ka da Brother zai yanke wannan d'anyen hukuncin".

"Rufamin baki ai duk halayyar ku iri d'aya ce ku ne masu uba mai kud'i to wallahi ina guje maku ranar nadama saboda wannan abin ba gata ne uban ku ke nuna maku ba", cikin fad'a sosai ta k'arashe maganar.

"Kin san dai Mum na d'ara Brother don bazan yi abinda ya aikata yau ba".

"Ku dai kuka sani, Allah ya ganarda ku daga ku har uban na ku don wallahi rayuwar ku kanta abar tausayi ce, don mutumen da baisan darajar d'an Adam ba yana cikin matsalar rayuwa, komai za kuyi ya kamata ku rik'a duba cancantar abin".

"Kullum game da tarbiyar ku tufka nake yi mahaifin ku na yiman warwara, a tunanin shi wannan gata ne".

"Mum tunda munsan girma da darajar ku ai ba muda laifi, dama ca akayi mu girmama iyayen mu".

"Sai akace ku taka duk wanda kuke so wannan shine dai-dai a cikin aya da hadisin Dad d'in ku?, wato mu ne mutane saura dabbobi ne a gurin ku".

"Mum ba kya ga newa ne, shi fa Dad raini da wulak'anci ne bai d'aukar mana ba shiyasa kike ganin tamkar wulak'anta mutane muke yi, amma ba hakan bane".
  "Mum fa su mutane ba ka iya masu idan kayi sake sai su ta ka ka son ransu".

Mugun kallon da ta bi ta dashi ne yasa ta ja bakin ta ta yi shiru.
D'aki Mum ta wuce tabar Saudat zaune a falon, ganin hakan ya sa ta bi sawun su Dad.

****

Sanadiyyar yau ta kama alhamis ba islamiya ya sa tun safe tana siyo masu koko suka sha ta hau wankin su ita da Baban ta.
   Bayan ta gama ne tayi shara ta tsaftace gidan, yau girki ta d'ora masu sanadiyyar tsakin masarar da Mama Inno ta ba su jiya wanda zai kai kwano uku.

Waje ta fita ta yi sa'a da yaran da ke tallan zogale dafaffe nan ta siyo ta had'o da d'an magi ta koma gidan.
     Faten tsakin masara ta yi wanda yaji zogale.

Sai da ta samu guri ta saka ma su Mama Inno faten ta kai masu sannan ta dawo gidan.

Ruwa ta ebo ta kaiwa Baban ta ya wanke hannun shi ita ma ta wanke sannan suka yi Bismillah suka fara ci.

Suna gama wa ruwa ta fara kai mai ya yi wanka sai da ya fito ta taimaka mai ya shirya yana ta sanya mata albarka sannan ta shiga wankan ta fito.

Sai bayan la'asar yau suka fita yawon su na bara, daka gansu tsaf dasu sai dai talauci dake barazana dasu.

Hakan ta gayar da mutanen gurin sannan suka nemi guri suka zauna, sai gab da magrib suka wuce gida inda ya tsaya gurin su Mal Inuwa itako ta shiga gidan su Salmat.

Sallah suka fara gabatarwa bayan sun k'are ne suka rik'awa juna bitar haddar su domin su k'ara daddak'awa.

"Salma zo ki lek'a daga waje ki kira Sagiru yakaiwa su Baban ku abincin su".

K'ur'anin ta ajiye ta fice bayan ta kira shi ne sannan ta dawo masu da nasu abinci d'akin, nan suka ci suka gama sannan suka gabatar da isha sai k'arfe tara sannan Zajla ta fita ta ja Baban ta suka wuce gida.

® *SDY JEGAL*

Dedicated to Anty ```Jidda``` ```Musa```.
[8:36PM, 11/7/2016] *SDY* *JEGAL*: ���� *ADALILIN GATA*����

                  *(4)*

*DAGA TASKAR Y'AR MUTAN JEGA*

®NWA
*NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*

Zaune suke saman dinning table suna breakfast sai tattaunawa suke yi akan lamarin company.

Sai da aka yiwa wayar shi Kira biyu ana ukun sannan ya d'aga wayar ya nufi hanyar d'akin shi, gaisawa suka fara yi sannan ya fara magana fad'a-fad'a had'e da ya mutse fuska.

"Kana sane da ce wa duk inda ake taro in har akwai Mata ba na nufar gurin, saboda haka kuci gaba kawai idan kun gama ma had'u, ka isar da sak'on taya murna ta zuwa ga Salis, in ya natsu zan kira shi".

Yana kai k'arshen maganar ya dak'ile wayar shi ya bita da wani kallo tamkar ta yimai wani laifi, gado ya fad'a domin ya d'an huta saboda ba mutum ne maison fita ba.

****

Kwanci ta shi asarar mai rai, yau ta ka ma Larba wanda Zajla sai gaban ta ke fad'uwa sanadiyyar tunanin da wuya Ustaz Lukman bai fitar da ita cikin masu karatun k'arshen sati ba.

Kamar kullum yau ma hakan ce ta kasance, bayan gabatar da sallahr azahar suka shiga class domin bitar haddar su saboda k'aratowar lokacin musabak'ar su.

Bayan an gama sallar la'asar ne aka fitar da mimbari da kujeru domin zama tsakiyar makarantar a gabatar da ire-iren abubuwan da ake koya masu.

Mutum uku cikin maza suka gabatar da yadda ake taimama da kuma sallar gawa, sai matan biyu da suka gabatar da koyar da alwala a aikace.

Zajla ce za ta gabatar da bayanin wankan tsalki da kuma addu'o'i.

Bayan ta yi basmala ta gabatar da sunan ta da Zajla Abubakar Zubair sannan ta fara da ce wa'.

"Shi dai wankan tsalki ya kasu zuwa kashi-kashi, akwai wankan janaba, akwai wankan haila, akwai wankan d'aukewar jinin bik'i (jego) da sauran su.

"Kamar yanda kuka sani su dai wad'annan abubuwan wanka iri d'aya ake yi masu sai dai niyyar su ce data ban-ban ta".

"Da farko za'a so mutum ya sa mu ruwan shi tsaftatacce, wa'anda kalar su bata canja ba, d'an-d'anon su bai canja".
  "Anan abinda ake nufi da kala ko d'an-d'ano shine kar mutum ya d'ebi ruwan Lipton ko ruwan wankin shinkafa ko ruwan da ke da gishiri yace wankan tsalki zai yi dasu".

"Da farko mutum zai fara wanke gaban shi, bayan ya wanke zai wanke hannun shi saboda najasar da ya ta6a, zai d'ebo ruwa har sau uku yazuba ma kansa, ya murza kansa har ruwan sukai k'asan kansa, daga nan zai yi alwala shud'i guda-guda sannan ya wanke 6angaren jikin shi na dama daga sama har zuwa k'asa, 6angaren hagu ma haka sannan ya game jikin sa da ruwa ya murza ko ina".

"An samu sa6anin wasu maluma da suka ce idan mutum ya wanke gaban shi zai fara gabatar da alwala, wasu kuma sukace sai bayan ya k'are wankan gaba d'aya sannan yayi alwalar. Allah masani".

"Addu'ar shiga kewaye
*(( Allahumma inni A'uzu bika minah khubithi wal khaba'ithi))*

"Addu'ar fitowa daga kewaye".
*((Gufranak))*

"Addu'ar mugun mafalki".
*((Allahumma inni A'udhu bika min sharri ma ra'aytu fii manaamee an yadurranee fii deeni wa dunyaay))*

"Addu'ar kariya daga azabar k'abari".
*((Allahumma innee As'alukar Jannah, wamaa k'arraba ilaiha min k'aulin wa amal, wa A'udhu bika minan naar wama k'arraba ilaiha min K'aulin wa amal, wa A'udhu bika min fitnatil mahya wal mamat wa min fitnatil k'abr wamin fitnatil masihid dajjal wamin Adhabin naari wasu'il maseer))*

"Addu'ar  neman ya fiyar sa6o.
*((Allahumma inni a'uzu bika an ushrika bika wa ana a'alam wa astagfiruka li maala a'alam))*

Gyaran muryar da akayi da speaker shi ya nu na mata alamar lokacin ta ya yi, speaker ta ajiye ta koma mazaunin ta.
     Kabbara ce ta biyo baya had'e da jin-jina mata akan abubuwan da ta gabatar.

Nan akayi salati ko wa ya ka ma gaban shi sanadiyyar gabatowar magriba, kowa da maganar (ZAZ) ya fita a bakin shi sanadiyyar add'o'in da ta yi tamkar itama Malama ce ba d'aliba ba.

® *SDY JEGAL*

Dedicated to Anty ```Jidda``` ```Musa```.
[5:56PM, 11/8/2016] *SDY* *JEGAL*: ���� *ADALILIN GATA*����

                *(5)*

*DAGA TASKAR Y'AR MUTAN JEGA*

®NWA
*NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*

"Gaskiya (ZAZ) kin kawo wuta sosai yau, kinji yanda kike rero addu'o'i tamkar Ustaz Yusuf?".

"Banson sharri wallahi, kina ji yanda murya ta ke wani rawa-rawa alamar tsorace nake. Ni fa shiyasa kika ga ko wannan musabak'ar da za muyi gabana ke ta fad'uwa saboda na k'i jinin karatu a cikin bainar jama'a".

"Tabbb ai wannan shafin mai ne wallahi, kina ganin yanda ake taro sosai idan lokacin musabak'a yayi. Kuma hakan da ake yi duk Larba anaso abin yabi jikin mune har mu saba mu daina jin tsoro", cewar Salmat.

"Ranar da duk Ustaz Lukman ya ji kina furta wannan (ZAZ) d'in a bakin ki kya yi bayani, saboda kinsan ya ce adaina kira na da hakan".

"Yo ai ba sai kin gaya min kina da mai tare maki ba, duk kauce-kaucen ku za ku fito kuyi bayani ne".

"Shin tsaya me kike nufi ne, ban fahimce kiba?".

"Kinsan dai ko kin 6oyewa ko wa soyayyar ku da Ustaz Lukman bai dace ni ki 6oyemin ba".

Cikin gwalo ido da wani cin birki tamkar mai tuk'in mota ta ja ta tsaya, mamaki kwance fal a fuskar ta.

"In har kin yarda kalmar "So" bata ta6a ratsawa tsakanina dashi ba, sai dai mutunci".

"Ke ce baki fahimci hakan ba, amma duk wanda ya yi mai duba na natsuwa idan kina gaban shi to zai hango son ki kwance a k'wayar idon shi".

"Allah yashirye ki, ke kika san wani abu "So" ni kam da saura na".
   "Ke ma za ki sani idan lokacin kisani yazo, wa yaga ana soyewa tsakanin Malami da D'alibar shi".

"Allah ni ko guntun namiji bai cikin tsari na ko Aure zan yi, na fison dogon namiji wanda zai yi guda da rabi d'ina".

Dundu Salmat ta kai mata had'e da furta, "makira kika ce baki san So ba kuma amma ga shi kina wassafa mijin da kike son Aure".
    "Shi ne sai aka ce maki wassafa ra'ayin ka shi ne So d'in?".. Yanzu bara in tambaye ki akawo maki gabjejen namiji wanda yayi hud'u d'in ki ya kika ga abin?", tana maganar ne had'e da dariyar k'eta.

"Bakin ki yasari d'anyen kashi muguwa kawai, Allah ya kiyaye ni".
   Dariya Zajlah tayi sosai akan yanda Salmat ke maganar had'e da ya mutse fuska tamkar ga mijin nan gaban ta.

Da hakan suka k'araso gida sannan suka gabatar da duk wani abu daya dace kafin Zajla taja sandar Baban ta su wuce gida.

****

Har gida yau suka kawo mai ziyara shi da Salis, bayan sun gayar da Mum suka fita gardener, saboda a al'adar shi in har yana gida indai ba bacci yake yi ba to nan ne gurin hutawar shi.

"Gaskiya (A.K.A) baka kyauta min ba, yanzu ace ayi birthday d'ina ko wa ya hallara kai baka je ba, kuma kana sane da ce wa duk duniya banda friends d'in da suka wuce ku kai da Imran".

"To ku ne da jaye-jaye kuce duk abinda za kuyi sai kun saka Mata a ciki shi ne birgewa a gare ku, ni ko in har hakan za ta cigaba da kasancewa to ina mai tabbatar maku za kuyi lamurran ku ba dani ba".

"Ni wannan abin na ka na d'aure min kai, zanga ranar auren ka da kuma matar da za ka aura, saboda wannan abin na ka ya yi yawa", ce war Imran.

Murmushi ya rik'a yi sama-sama wanda har fararen hak'oran shi na bayyana had'e da dimple d'in shi.

"indai ku kuka ta shi auren Allah sanya alkhairi don kunsan ba dani ba a y'an dinner da sauran su, zan dai je d'aurin aure shi ne na mu".

Kallon da suka bi shi dashi ne ya sa ya yi saurin kauda kan shi yana dariya k'asa-k'asa.

"Ka ma mayar damu wasu sha ka wuce za ka gani ne. Na ma manta in gaya ma Lubnah ta ce in ba ta number d'in ka".

Mugun kallon da ya yimai ne ya sa ya fahimci amsar da yake nufi zuwa gare shi.

"Baiwa wata Mace number ta na nufin rabuwar mu ta har abada dakai, ka sanni kasan waye ni. Duk cikin contacts d'ina number Mace biyu nake da, Mum da Lil Sis".

Cikin 6acin rai ya mik'e ya tattara wayoyin shi ya nufi hanyar shiga gida, duk yanda ya so tsayar dashi don ya nuna mai wasa yake yi abin yaci tura.
   Bayan ya shige ne gidan Imran ya kai duban shi ga Salis had'e da hararar shi sannan ya furta.

"Sai ka ta shi mu fice tunda ka takaro zuciyar manya". Dariya sosai Salis ya yi had'e da furta.

"Ni fa suk'uwar shi dariya take ba ni, da abin 6acin rai da wanda bana 6acin rai ba za kaga ya had'e fuska ala dole shi fushi yake yi".

"Allah wataran da gayya nake tsokanar sa saboda inyi dariya".

"Don kasan duk rintsi yana tare damu ne, ko ya yi fushi dole yasauko shiyasa kake mai hakan", ce war Imran.

Hakan suka had'a nasu da nasu suka fice saboda sanin in kwana za suyi gurin bazai kuma kula su ba sai ranar da ya sauko daga zuciyar.

® *SDY JEGAL*

Dedicated to Anty ```Jidda``` ```Musa```.

Tuesday 1 November 2016

KOMAI AKA SAKA MA RANA

������ *DUK ABINDA AKA SAKA MA RANA*������

      *ONE TO END*

*DAGA ALK'ALAMIN Y'AR MUTAN JEGA*✍��.

Wayar tace ta d'aga cikin sauri had'e da furta "don Allah kuyi hak'uri ga munan fitowa, dama Issuhu muke jira yazo kuma gashi nan ya iso".

"Assy! Assy!! Assy!!!".

Sai ana ukun ne ta kar6a had'e da fitowa daga d'akin rik'e da riga a hannu.

"Kina nufin ma ko shiryawa baki yi ba?, to wallahi yanzu Ramu ta kira kan cewa an kammalu mu kad'ai ake jira".

"To ku kai kaya napep kamin in k'arasa shiryawa".

Issuhu ne ya taimakawa Hauwa suka saka kayan a napep sai ga Assy ta shirya ta fito, daga nan suka yi bankwana da iyayen su suka d'auki  hanya sai school of health.

Da suka isa gurin sun sha surutun mutane kan ce wa sun tsayar dasu musamman Maryam.

"Kawai kice kin matsu baki je tsafe ba shiyasa kika ta damun mu da kira kan cewa mu fito hakanan", cewar Assy.

"Me zai sa in matsu don zanje dajin Allah? Ke fa ni dazan fito daga gida har da hawaye na in bakiji tsoro ba".

Da hakan dai aka cika bus biyu d'aya ta maza d'ayan ta mata suka kama hanya sai tsafe.

Bayan sun sauka ne sai kallon kallon suke yi saboda mamakin dajin Allah da aka kawo su, hakan dai aka raba masu guri kowa ya d'auki kayan shi.

Hauwa, Assy, Maryam, Ramu sama aka basu masauki, sai sun kalli kayan da suka jibgo su kalli yanda zasu hawa su kai su sama ga uban gajiyar da suka kwaso.

Dole hakan suka jure suka rik'a jidar kaya suna kai masaukin su, bayan sun had'a komai ne suka dawo jiganiyar d'ibar ruwa suna kai saboda su samu na lalurar su.

Hauwa har da guntun hawayen ta tana furta "wannan bak'ar wahala ta yi yawa, tun ba'aje ko ina ba har na fara kewar iyaye na, in gida ne ya za'ayi nayi wannan wahalar".

Assy ce ta bita da harara tana furta "Dama ai ko gidan baki da kata6us don ba kowane aiki kike iyawa ba".

Ramu ce taja Hauwa suka wuce da robar ruwan da suka ebo.

Maryam da Assy suka mara masu baya. Bayan sun shiga masukin sune aka koma shawarar me za'aci.

Ga dai spaghetti, indomie, cus-cus da 6ula har da miyar su da dallaki da sauran kayan tarkace.

Nan dai suka yanke shawara suka ci 6ula, sun kwanta kenan Hauwa ta kai duban ta zuwa gare su.

"Me kuke nufi bazaku tashi muje d'akin karatu ba kuka samu guri kuka kwanta?".

"Duk wannan gajiyar da muka jibgo za kice muje karatu, Allah yakai ki lafiya mukam Asuba ta gari".

Ganin sun yi kwanciyar su yasa ta kwashi kayan karatu ta fice daga d'akin.

Ko minti ashirin batayi da fita ba sai gashi ta rik'a jin bacci dak'yar ta samu wani ya raka ta ta koma masauki.

****

*BAYAN KWANA BIYU*

Yau tun safe suka tashi saboda yau ne zasu fara exam d'in da ta kawo su a garin na tsafe. Da hakan suka shiga paper one da safe sai paper two bayan azzahar.

Ranar alhamis suka fara practical da hakan aka rik'a tantance su d'aya bayan d'aya ana masu signing.

Kuka su Assy suka hango Hauwa nayi, koda suka isa gurin ta da tambayar me ke faruwa kuka ta k'ara saki.

"Kayan practical d'ina aka sace, na yi nema bangan su ba".

"Ke dai Allah ya yi maki sauk'in saunan ci", ce war Assy.

Gurin wani malami ta je tana gaya mai ansace mata kayan practical, ko kallon ta bai yi ba.

Wani Malami ta hango zaune ta tunkare shi  tana hawaye tana gaya mai.

"Kin tabbatar an maki signing a takardun ki?".

"Eh wallahi Malam anyimn".

"To je ki ba matsala insha Allah".

Da hakan suka fice zuwa masaukin su suka dafa cus-cus sukaci.

Ranar Friday suka yi viber suka k'are, daga nan ne suka fara shirya kayan su domin haramar dawowa gida. Bayan sun kimtsa ne sai ga bus d'aya ta zo ta Maza amma ta Mata bata zo ba.

Da hakan aka kira wayar shi yake gaya masu motar shi ta samu matsala, shi ko direban bus d'in Maza ya matsa kan cewa sauri yake yi saboda yana da lodi zuwa Abuja.

Dole matan na gani Maza suka wuce suka bar matan daga Malamin da aka had'osu dashi sai Ahmad daya jira su.

Suna nan zaman jiran isowar direba har y'an tsafe da aka turo exam garin Jega suka koma.

Nan akayi waya da H.O.D d'in su sannan suka biyo motar da ta ajiye y'an tsafe d'in suka dawo gida.

Basu iso Jega ba sai wurin k'arfe tara na daren Juma'a, nan suka yi waya gida aka tura Umar ya d'auko su daga health zuwa gida.

Ranar assabar ne ni Sdy, Anty Ruky, Sis Nafee, Sis Blkisu muka kammalu gida domin taya su Assy murnar k'are makaranta da fatar fitowar kyakkyawan result.

Lallai tabbas *DUK ABINDA AKA SAKA MA RANA ZAI ZO IN HAR DA RAYUWA*

(Duk abinda ke cikin wannan gajeren littafin gaske ne ya faru, na yi shine domin nishad'antarwa da kuma taya K'anne na murnar kammala karatun su.)

Fatan alkhairi da fatan samun nasara zuwa ga k'anne na.

Na sadaukar da wannan gajeren littafin gare ku.
Asiya Labaran
Hauwa Labaran
Maryam Abubakar Muhammad
Aisha Bello (Ramu).

Gaisuwar ta ka ce da babbar murya Ahmad Abdulkareem.

*SAKON GAISUWA DAGA HAUWA AND ASSY*

All praise be to Allah the most gracious the most merciful.
Our special thanks to our parents for their personal support and attention towards our studies (May God continues to guide you).
Also special thanks to u our luvly brothers and sisters for ur help����.
Also special thanks to u our friends.
A special thanks to the staff of medical laboratory technician and including the staff of health technology jega,kebbi state.
The long journey ends today, those that we are still going to meet again I pray that we shall meet in peace not in pieces missing you all our *COURSE MATE*������.
And finally to God who made all the things possible to us till the end.
     *Your's Asiya and Hauwa'u Labaran Jega*.

*BY SDY JEGAL*

Tuesday 18 October 2016

BAHIJJA 105-115

[8:24PM, 10/17/2016] Sis  Hauwa: �� *BAHIJJA* *105*- *110*��


Koda aka je da ita asibiti duk bata San in da take ba, nan suka yi aune-aunen su Dr Musa yace gaskiya sai an fita da ita Dubai.
Nan take Dad yasa aka yi biza uku ta tafiya, da malam salisu ya Gan ta sai da yayi kuka sosai, yace lallai tabbas rayuwar duniya ba bakin komai bace.
KO kamin su wuce Dubai sai da yaje gidan su Lateefa tak'i Bari ya Gan ta ta shige d'aki ta rufe, abin har ya Fara bama Umma haushi tace ma Shureim ya je kawai ya k'yale ta.
Hakan suka d'unguma da Gwaggo sai Dubai, har suka shigo k'asar Bahijja kuka take yi saboda tausayin halin da Gwaggo take ciki,  nan Shureim ya Kama musu d'aki biyu su d'aya Baban Bahijja d'aya.
Bayan ya ajiye su masauki ne aka wuce da Gwaggo asibiti, bayan gwaje-gwajen su suka ce dole d'ayar k'afar wadda k'wauron ta ya tartse sai an yanke ta, d'ayar kuma za ayi Mata d'orin kariya na asibiti, hakan Shureim ya yi duk abinda ya Kama ta sannan ya koma masauki saboda baije da Bahijja ba akan kukan da take yi.

**********   ********

Yau kwanan su Bahijja uku da tafiya Mum ta shirya taje gidan su Lateefa.
Tana shiga suka gaisa da Umma tace gani nazo bikon y'ata.
Umma tayi murmushi tace ke kike wahalda kan ki akan wannan sha-sha-shar kawai Ku saka Mata ido har ranar da duniya ta yimata fad'a.
Mum tace ai ba ayi haka ba, suna maganar ne Shema'u ta kawo ma Mum kayan motsa baki, bayan ta ajiye ta durk'usa ta gaida ta.
Mum ta amsa tace shiga ciki ki Kira min Lateefa.
Suna cikin hira ne sai ga Lateefa ta iso nan ta gaida Mum ba yabo ba fallasa.
Mum tayi murmushin su na manya tace Lateefa har yanzu ba agama fushi Dani ba?
Nan ta had'e rai tayi shiru bata ce komai ba.
Mum tace Lateefa kiyi hak'uri shi aure nufi ne na Allah, kuma wannan matar kinsan ba Shureim ya furta cewa zai aure ta ba Dad d'in Ku ne ya yi wannan had'in, kiyi hak'uri ki bar ma Allah kuma kinsan waye Bahijja bata da matsalar zama kiyi hak'uri kinji y'ata.
Tace to shikenan Mum sai na shirya Zan koma.

****  ****  ****  ****

A can Dubai kuma an yi aiki cikin nasara saura jiran shan magani da sauran warkewar Gwaggo.
Kullum da safe zasu je su duba jikin Gwaggo sai marece su koma masaukin su.
Kullum Bahijja kesa towel ruwa ta shafe ma Gwaggo jikin ta, sannan ta zauna ta rik'a ba ta abinci.
Koda Shureim ya dawo daga masallaci ya taradda Bahijja na sallah, bayan ta idar ne suka zauna suka ci abinci suna k'arasawa yakai duban shi zuwa Gare ta yace Sister shine ba ko sanarwa.
Fahimtar inda ya dosa yasa ta soke kan ta.
Yace na kusa fitar da wannan kunya taki saboda tana takura min.
Nan tayi murmushi tace yaya ka Kira Anty Lateefa?
Yace Antyn ki bata sauko ba har yanzu tana fushi kin k'wace Mata sankacecen saurayi.
Nan take ta zare ido dai-dai ya tada kan shi sai suka had'a ido ita ko ta sunne kan ta tana murmushi.
Hakan ya taso ya rik'a hannun ta ya mik'ar da ita ya yi mata rad'a cikin kunne, da sauri ta fizge hannun ta tayi cikin d'aki.
Yana shiga yace taje tayi alwala zasu yi sallah, hakan tayo alwala sai gaban ta ke dukan uku-uku.
Bayan sun gama ya yi Mata tambayoyin da suka shafi addini kuma tana da ilmin ta gwargwado.
Hakan taje tayi wanka ta feshe jikin ta da turare, shima hakan.
Suna kwanta wa ya Jan yota saman k'irgin shi ya yi Mata kyakkyawar runguma ya ja masu bargo.
(Nidai Jegal nace Allah ya bada d'an Dubai, *LOLX*)

~~~~~~~~~~
~~~~~~~~~~

*WASHE* *GARI*

Yana tashi daga bacci yaje yayi wanka sai da yayi sallah sannan ya had'a ruwa masu d'imi yazo ya yaye bargon da ta rufa dashi ya sunkuce ta sai toilet.
Shi ya yi Mata wanka ya gasa ta, tana cewa nidai yaya banaso tana soke Kai.
Sai da ya gama sannan ya d'auko ta ya nad'e cikin towel ya ajiye ta ya d'an fita.
Ko kamin ya dawo ta lalla6a tayi sallah har ta shirya.
Ashe gurin Baban ta ya shiga suka d'an ta6a hira saboda k'a idar asibitin da aka Kai Gwaggo Mai jinya bai kwana can.
Yana shigowa ya iso ya zauna gefen gado yakai dubanshi zuwa Gare ta sai kuma ya Jan yota ya Kai Mata kiss ita ko duk kunya ta ishe ta.
Yace Heeja Ina son in yi maki wata tambaya d'aya.
Tace Ina jin ka yaya, tana Mai Kai duban ta zuwa gare shi.
Yace ya akayi na same ki budurwa bayan kuma kin yi aure sama da shekara biyu sannan Allah ya kar6i ran margyayi?
Nan idon ta suka yi rau-rau tamkar ta yi kuka.
Ya k'ara Jan yota saman jikin shi yana bubbuga bayan ta cikin rarrashi yace kar kiyi kuka.
Tace ka bari in mun yi breakfast mun je dubo jikin Gwaggo mun dawo Zan gayama.
Ba hakan yaso ba saboda ya matsu yaji ya akayi hakan ta kasance, sai dai baison takura ta.

(Nima dai na matsu in ji yadda hakan ta kasance����)


© *SDY* *JEGAL*
[8:24PM, 10/17/2016] Sis  Hauwa: �� *BAHIJJA* *110*- *115*��

Tana d'akin ta Shema'u k'anwar ta ta shigo tace Anty kin yi bak'i.
Tace daga Ina, nifa banson takura wallahi.
Ta ce Mata inaga kamar wannan mak'ociyar ki.
Tace to ki shigo dasu, nan ta fita ta shigo dasu.
Suna shigowa taga cewa maman Zahra ce da Mum zee, nan ta tashi ta taryo su cikin murnar ta da sakin fuskar ta.
Nan Shema'u ta kawo musu kayan motsa baki da abinci.
Bayan sun gaisa Mmn Zahra tace shikenan kin gujemu ko waiwaye babu.
Tayi murmushi tace ba gamu tare ba yanzu, kuma muna waya.
Mum zee tace wallahi baki kyauta ba wa yace maki ana tashi gidan miji saboda kishiya, shifa lamarin duniya sauk'i Gare shi sai Wanda ya wahalda kanshi.
Kuma kishiya abokiyar zama ce don wani lokaci zaka ci amfanin ta itama zata ci naki.
Mmn Zahra ta kar6e tana Mai cewa har fa kullum kina yabon halayen Bahijja kuma kin fad'a da kan ki cewa kullum kina yi Mata addu'a Allah ya bata miji nagari.
In kin manta in tuna maki har cewa kika yi da kina da d'an Uwa namiji da kinsa ya aure ta.
Me yasa ba zaki yarda cewa mijin ki shine mafi alkhairi a gareta ba.
Yanzu mum zee ba zata zama ishara gareki kisan cewa ba duka aka taru aka zamo d'aya ba, gasunan suna zaman su lafiya tamkar ya da k'anwa.
Nan Lateefa ta saukar da wata nauyayyar ajiyar zuciya, tace nifa kar kuga abinda ke tayar min da hankali tamkar Amarya ta shigo cikin gida ta nemi fitar da uwargida.
Wata ma in kina da yara zata nemi hanyar da zata bi ta wulak'antar da su ga ubansu.
Mmn Zahra ta kar6e tana Mai cewa yarda kika San amare da tasu matsalar to ko uwayen gida suna da tasu matsalar, saboda wata uwargida ba zata fitar da Amarya ba amma wallahi zata yi silar wulak'anta ta yarda ko y'ar aiki zata fita daraja, ke dai kawai muyi fatar Allah yadatar damu da kiyoshi na gari masu zuciyar imani.
Mum zee ta kar6a da ameen tana Mai cewa kuma gaskiya kinga wani lokaci uwayen gida Nada tasu matsala.
Abu na farko zaki ga wata da zarar ance za ayi Mata kishiya to zaki ga ta Fara hauka tana sakin maganganu da zasu fita har sukai ga kunnen amarya kinga girma ya fad'i.
Abu na biyu azo ayi aure uwargida ta k'i kama girman ta, shima hakan na kawo raini tsakanin zama saboda kin sake taga makwancin ki.
Amma gaskiya muddin kika rik'e girman ki koda Amarya ta shigo bazata raina kiba kuma in kin dace da tsayayyen miji saboda ko su da tasu matsala.
Mmn Zahra tace yanzu miye ribar ki kinfita kinbar gida, kuma hakan bai hana auren ba don yanzu haka suna Dubai shida Amarya, kinga kuwa kin d'aga musu k'afa susha amarcin su hankali kwance.
Nan tashin hankalin Lateefa ya k'aru saboda batasan sunyi tafiyar ba, Umma ta hana agaya Mata saboda ko y'an gidan ta rage mu'amala dasu ko yaushe tana d'aki.
Nan take ta mik'e ta lalabo layin ta data d'ebe ta saka shi a waya saiga text message d'in shi na shigowa na ban hak'uri, sai ga wasu zafafan hawaye na sauko wa daga idon ta na tausayin kan ta.
Nan dai suka rarrashe ta har ta sauko kuma tayi masu alk'awari zata ba Kimba mamaki don zai dawo ya taradda ita d'akin ta.

*******************

A can Dubai kuma su Shureim sun shirya sai asibiti domin su duba jikin Gwaggo.
Suna shiga Bahijja ta had'a Mata tea Mai kauri tasha sannan ta jik'a towel ta shafe Mata jikin ta.
Nan Gwaggo ta rik'a kuka tana cewa y'ar Baba ki yafemin na cuce ki na zalunce ki yanzu gashi dake da mijin ki ke wahala dani.
Malam yace ki daina wannan kukan bayada fa'ida.
Tace malam dole in yi kuka nan ta rik'a zayyano irin cutar da ta rik'a yima Bahijja har zuwa yanzu data so 6atar da ita Allah ya nuna Mata abinta.
Ta d'ora da cewa ko mahaifiyar ta nice nayi silar zuwan ta barzahu, saboda ciwon ta na tashi malam ya fita kasuwa ni na saka filo na danne ta saida ta daina numfashi.
Nan Bahijja ta fad'i sume, malam ko yayi mutuwar tsaye inda Shureim ya bita da kallon tsana ji yake yi tamkar ya k'arasa gundule k'afar ta d'aya.
Sannan ya durk'usa yana jijjiga Bahijja da k'arfi yace _Heeja_.


© *SDY* *JEGAL*

BAHIJJA 95-110

[8:24PM, 10/17/2016] Sis  Hauwa: �� *BAHIJJA* *95*- *100*��

Lateefa ta shirya ta dawo falo tana jiran shi, yana fitowa suka wuce, saboda zai sauke ta gidan su Muftah shiko zai wuce wurin d'aurin aure.
An d'aura auren *MUFTAH* da matar shi *BILKISU* *BILYAMIN* sai dai fatar zaman lafiya tsakanin su.
Sai zuwa dare da aka Kai Amarya Shureim ya rako ango sannan ya wuce da Lateefa.
Nan yake yiwa Muftah sharri kan cewa sai sun zo barka nan da wata tara, saboda naga zumud'in naka yayi yawa.

********   *********

Yau tun safe Lateefa ke Kai kawo a gidan, tana ba Bizzy umurnin abinda zata dafa.
Can ta shiga d'akin Shureim yace wai yau me ya hana ki zama haka?
Tace ka manta na gaya ma Sis zata zo muna yini yau.
Yace OK shine kike ta rawar Kai haka, ni na zata daga wata k'asa za kiyi bak'i, saboda naga wataran baki tashi daga bacci sai k'arfe goma, amma yau kece da tashi tun takwas.
Tayi murmushi tace Kimba wallahi Ina ji da Sis Bahijja ne tamkar k'anwata Shema'u, naga Kai ko tausaya Mata baka yi.
Nan yayi murmushi yace asha aiki lafiya, koda bak'uwar taki ma sai dai taci girkin y'ar aiki ya bita da gwalo.
Gane cewa tsokana yake ji yasa ta k'yale shi ta shiga wanka.
Koda ta fito ta shirya sai ta dawo falo ta zauna, bata fi minti goma da zama ba sai ga Bahijja ta iso ita da k'awar ta Yagani.
Hakan ta shek'o ta rungume Bahijja sai murna take yi, tace ma Yagani bismillah zauna mana.
Hakan suka zauna tasa Bizzy ta cika masu wuri da kayan tand'e-tand'e da lashe-lashe.
Suna zaune suna hira ne sai ga Shureim ya fito cikin shiga ta alfarma, ya saka k'ananan kaya ga sajen shi ya kwanta luf, ya had'u iya had'uwa ga kwarjini da ya cika fuskar shi.
Nan Bahijja ta durk'usa har k'asa tace yaya ina wuni.
Ya amsa da k'alau ya d'ora da cewa ya karatun, ya kuka baro Mum?
Tace k'alau Alhmdulillah.
Nan ma Yagani ta gaida shi, ya amsa yace to akula da karatun.
Nan yakai duban shi ga Lateefa yace to ni zan fita, nan ta rakashi sai da ya tada mota sannan ta dawo.
Bayan su Bahijja sun ci iya abin da zasu ci, nan ta jasu har bedroom d'in ta suna ta hira, Lateefa tace yaushe zaku gama karatun?
Tace nan da shekara guda.
Jin kiran azzahar ne yasa suka tashi domin sauke farali.
Bayan sun gama sallah ne Bahijja ta shiga kicin ita da Yagani ta had'a masu abincin dare, sannan suka kimtsa zuwa tafiya gida.
Lateefa tace kiyi hak'uri Kimba ya dawo sai ya sauke Ku nima inaso in bishi in gaida Mum.
Da k'yar ta samu suka zauna, sai da Shureim ya dawo yaci abinci yayi wanka ya canza kaya yayi shigar manyan kaya.
Nan ya kwashe su suka wuce, Yagani ya fara saukewa Lateefa ta bata ledar kayan Shafa tayi godiya sannan suka wuce gida.
Nan suka zauna gurin Mum suna ta hira sai daga baya suka wuce.

**********   **********

```BAYAN``` ```SHEKARA``` ```D'AYA```

Yau ne Bahijja suka gama exam d'in su ta k'are health, daka dube su zaka San cewa suna cikin farin ciki.
Bayan fitowar su da kar6ar address d'in juna kowa ya Kama gaban shi.
Hakan kowa yaje gida cikin farin ciki da murna.

_BAYAN_ _KWANA_ _UKU_

Kamar yadda suka yi alk'awari da Mum kan cewa in ta gama karatu yazo ya wuce da ita.
Hakan yasa yau malam ya zo domin zuwa da Bahijja gida, koda yazo ya taradda Baban margyayi ma yazo hakan suka zauna aka tattauna rayuwar yau da kullum.
Cikin hakan ne Dad yace malam salisu Zan k'ara Neman wata alfarma Karo na biyu zuwa gare ka.
Malam yace haba Alhj wace irin alfarma ce wannan, na gaya ma babu shamaki tsakanin mu.
Ya yi murmushi yace d'an ka Shureim zaka bawa Bahijja aure.
Baban margyayi yace Alhj ya akayi kasan abinda ke cikin zuciya ta, dama wannan maganar ce ta kawo ni.
Nan dai suka yi maganar aka aje d'aurin aure sati guda masu zuwa.
Malam yace to zai je da Bahijja gida sai ranar alhamis zata dawo.
Hakan suka d'ungu ma sai Kimba, saida suka sauka malam yake gayama Bahijja meke faruwa.
Tace Baba don Allah ka taimakeni Ku janye wannan maganar, bazan iya auren Yya Shureim ba, innayi hakan na yaudari Anty Lateefa.
Yace kiyi hak'uri y'ar Baba ba yin kaina bane, kuma kinsan mutanen nan sunfi k'arfin komai a wurin mu.
Gwaggo tace kiyi hak'uri shi aure nufi ne na ubangiji, nan suka rarrashe ta sannan ta tashi ta koma d'aki.
Tana shiga d'aki ta fasa kuka maicin rai, tace mutuwa Mai yankan k'auna, yanzu da wane ido Zan kalli Anty Lateefa naje Mata matsayin kishiya.
Tana cikin tunanin ne taji Gwaggo saman kan ta, tace shegiya mayya kin lashe musu yaro ya mutu yanzu kin koma ga d'an cikin su.
To wallahi Bari in gaya maki ko Zan tafi tsira ra ba zaki aure shi ba, makwad'aiciya Mai idon cin nera ta Kai Mata rank'washi sannan ta fita.

Bayan taje ziyara dangin innar ta, kuma taje gidan su margyari har gidan lantana sai da taje.
Yau Mum ta turo direba ya koma da Bahijja, sannan tasa aka d'auko Mata Lateefa.
Nan ta had'a su tana yi masu nasiha sannan ta furta ma Lateefa abinda ke faruwa.
Dama an gaya ma Shureim ya amsa ba yabo ba fallasa sai dai fargabar had'uwar shi da Lateefa.
Lateefa ta bi Mum da ido tace bangane ba.
Mum tace saura kwana biyu auren Shureim da Bahijja.
Idon sun k'ank'ance ta bud'a baki zata yi magana kome ta tuna, sai ta zabura ta nufi hanya tamkar zararra.
Mum na kiran ta ko waiwayo ta bata yiba da saurin ta tafita daga gidan.
Bahijja ta rik'a kuka maicin rai tace Mum kiyi hak'uri ki janye maganar nan, kin ga Lateefa ba zata ji dad'i ba.
Mum tace mu mukasan dalilin wannan had'in, in kema zaki bijiremin ne kamar yada Lateefa ta yimin to bisimillah, ta tashi ta wuce d'akin ta tabar Bahijja nan.

Yau ne mutane suka shaida auren
_SHUREIM_ _SULEIMAN_
              *DA*
_BAHIJJA_ _SALISU_
A garin Kimba, Allah ya basu zaman lafiya.

(Masoyan Bahijja Ku fito Ku taya ta zaman kishi da Lateefa, _lolx_)


© *SDY* *JEGAL*
[8:24PM, 10/17/2016] Sis  Hauwa: �� *BAHIJJA* *100*- *105*��

Duk mutanen k'auyen Kimba sun shirya an yi mota uku har da dangin innar Bahijja sun nufi jega gurin auren Bahijja.
Amma koda aka yima Gwaggo magana kan a shirya sai tace su tafi zata zo daga baya sai ta kar6oma d'iyar ta wasu abubuwa.
Bayan sun wuce Gwaggo tayi gurin bokan ta, tace boka d'an dugaji na rasa ya Zan yi da wannan shegiyar yarinya nidai yanzu na yarda akashe ta ko a 6atar da ita.
Hhhhhhhh dama tun farko nace ki bari ayi hakan kika k'i, amma yanzu tunda kin amince Zan baki wasu ruwa ki k'ok'ar ta kamin a fita da ita zuwa gidan mijin ki saka Mata su cikin ruwan wanka, hakan zai yi sanadiyyar 6acewar ta har abada.
Da sauri ta tari mota tayi sa'a da saura mutum guda ta fad'a suka kama hanya.
Har sun kusa isowa jega wata babbar mota tabi ta kan motar su, nan aka kwashe su sai asibiti wasu sun rasu, wasu kuma sun ji rauni.

*********   ***********

Lateefa na shiga gida ta fad'a saman jikin mamar ta sai kuka take yi.
Umma tace lafiyar ki kuwa, wa ya rasu?
Da k'yar tayi shiru ta gaya ma Umma meke faruwa.
Nan Umma taja dogon tsaki tace in zai yi aure shine me, dama cewa aka yi dake kad'ai zai zauna sha-sha-shar banza da wofi.
Kuma ni hakan yayi min dai-dai sai shegen kishi amma bakisan ya zaki gyra tumbin mijin ki ba, dama nasan hakan zai faru komi dad'ewa.
Tana cikin yi Mata fad'an ne sai ga Abban ta ya sauko nan yake tambayar meke faruwa.
Umma ta yi Mai bayani nan ya Fara fad'a yace Lateefa ta tashi ta shiga dakin ta, ya d'ora da cewa ba inda zata je yaje ya zauna da amaryar shi.
Umma ta Kai duban ta zuwa gare shi tace ina fatar ba kashe ma y'ar ka aure zaka yi ba, gaskiya kana nuna ma yarinyar nan gatan da bai dace ba.
Yace ko ke da kika haife ta nace Zan yima kishiya sai anga tashin hankali ballan tana ita, ai kishi a jinin Ku yake.
Nan ya sa Kai ya fice yana ta faman fad'a.

**********   ***********

Can gidan su Shureim kuwa an ji Gwaggo shiru kuma ba waya take da ita ba har k'arfe goma bata zoba sai kawai aka yanke hukuncin aje akai amarya d'akin ta k'ila gwagg ta fasa tahowa.
Hakan aka d'unguma Kai amarya, ciki kuwa har da Blkisu matar Muftah su lantana da Hindatu k'anwar margyayi.
Nan dai aka yi Mata hud'uba kowa ya wuce sai Blkisu da Aisha Yagani.
Sai k'arfe goma sha d'aya ango ya shigo shi da Muftah nan ya had'asu ya k'ara yi masu nasiha kan hakk'in miji akan matar shi da kuma hakk'in Mata akan mijin ta.
Bayan yayi addu'ar zaman lafiya ya sa matar shi gaba, Shureim yace su sauke Yagani gida, bayan sun wuce ya rufe gida ya dawo ya taradda Bahijja ta wuce d'aki.
Part d'in shi ya wuce ya watsa ruwa yasa kaya marar nauyi sannan ya fito ya d'auki kayan da ya shigo dasu ya shiga d'akin Bahijja.
Koda ya shiga tayi wanka ta saka kayan bacci, nan ya aji ye kayan yaje kicin ya d'auko plate da cups ya dawo d'akin, ya zuba komai yace ta sauko suci.
Cikin sanyin muryar ta tace yaya na k'oshi.
Yace ki sauko kici ko kad'an ne, ganin cewa bata iya yimai gardama yasa ta sauko, kuma tun fil azal nauyin shi take ji sosai.
Hakan suka ci suka k'oshi, sannan ya umurce ta da ta tashi tayi alwala suyi nafila.
Nan ta rik'a soke Kai ta kasa magana, jin ya maimaita maganar ne yasa ta furta period take.
Hakan yaji ba dad'i duk da bai k'udurta ma ranshi wata doguwar mu'amala tsakanin su.
Hakan suka kwanta saman shimfid'a guda ya janyo ta ya manna saman k'irjin shi.

*********   ************

Lateefa kuwa tana gidan su sai juyi take yi saman gado zuciyar ta tamkar zata k'one saboda suya.
Anyi-anyi ta koma d'akin ta tace Sam ita ta gama da Kimba don bazata iya had'a shimfid'a da shiba yaje ya had'a da wata ba.
Ko su Anty Nafeesa sun zo auren Shureim duk yada ake bada baki sun bata kan ta koma d'akin ta amma Abu ya faskara.
Daga baya ma munafukai ta rik'a ce musu tana cewa har da kwaso jiki suzo aure don za ayi Mata kishiya, kuma kishiyar ma data rik'a tamkar k'anwar ta shema.
Anty Nafeesa tayi murmushi tace koda auren ki ko babu dole muje ma Mum auren Shureim.
Duk yada ake bada baki Shureim ya yi amma tak'i sauraren shi, ko ya Kira waya bata d'auka, yayi text message har ya gaji ba reply.
Kuma ko yazo gidan su data jishi take rufe k'ofar ta.
Shi kuma Abban ta yace ba zai takura taba abar ta sai ranar da ta sauko da kan ta.

Yau da safe aka yi bincike Gwaggo bata Kimba bata Jega nan hankalin mutane ya tashi kan rashin takamemen ina take.
Shureim na breakfast shi da Bahijja yana tsokanar ta sama-sama kan cewa abinci ne bata ci sosai shiyasa tak'i yin k'iba.
Ita ko sai murmushi take yi tana soke Kai, cikin hakan ne wayar Shureim ta hau ruri koda ya duba Dad ne ya Kira shi.
Bayan ya d'auka suka gaisa yake ce Mai yayi sauri yazo yana Neman shi sai ya kashe wayar.
Gaggauce ya gama breakfast ya d'auki key d'in mota har ya Kai k'ofar fita daga falon ya waiwayo idon su suka had'e sai ta soke Kai tana murmushi.
Yace Mata dubo kigani, tana tayar da kan ta ya yima hannun shi kiss ya hura Mata iska ya wuce.
Cikin ran ta tace Ashe haka yaya yake da dad'in zama.
Yana shiga ya gaida iyayen shi, nan aka Kora Mai abinda ke faruwa take ya Kira Muftah yace ya bincika Mai asibiti koda akwai masu hatsari, hakan ya Kira sauran doctors na asibitoci da dama yana basu cigiya.
Ba afi minti goma ba sai ga kiran Muftah yace Mai akwai su nan asibitin su kuma ance akwai y'an Kimba ciki.
Nan suka d'unguma shi da Mum da Dad sai asibitin, cikin bincike ne aka gano cewa tana cikin masu rai sai dai k'afar ta d'aya ta karye d'ayar kuma k'ashin k'wauron ta duk ya tartse fuskar ta duk taji rauni.
Nan Dad ya Kira direba yace yaje Kimba yazo da Baban Bahijja, shiko Shureim ya Kira wani friend d'in shi asibitin F.M.C Birnin kebbi kan cewa yanzu zai turo gwaggon shi aduba ta.

(Fan's na gode sosai da kulawar ku, wasu sun Kira sun yimin ta'aziya, wasu sun yimin ta p/chart, wasu ta groups na gode sosai Allah ya bada lada.)

© *SDY* *JEGAL*

Monday 17 October 2016

SANADIN KUNCI 71-80

[7:28AM, 10/17/2016] *SDY* *JEGAL*: �� _SANADIN_ _K'UNCI_ 7⃣1⃣/7⃣2⃣��

*BAYAN SATI UKU*

An sallamo Umma daga asibiti kuma ta samu sauk'i alhmdulillah, je kaga zama tsakanin ta da Ammi tamkar su had'iye juna idan ka gansu ba za ka ta6a cewa sunyi zaman rashin fahimta a baya ba abin gwanin ban sha'awa don ko yaran su in har ba ka sani bane ba za ka tantance yaran Umma da Ammi ba.

****

6angaren Haydar kuwa manya sunje gidan su Mela har an saka lokacin aure wata biyu masu zuwa, inda suke gina soyayyar su cikin jin dad'i da walwala tamkar su had'iye junan su.

****

Yau ne Ammi ke ta hada-hadar zuwa Bk domin ta dubo tsohon ta, inda suka yi aje kan ce wa Mubarak zai bi ta domin maganar shi da Mama Baraka.

Hakan suka shirya sai Bk inda ta tarar da Baban ta cikin k'oshin lafiya sai abinda ba za'a rasa ba na tsufa.

Bayan sun huta ne Ammi ta shirya duk ta kaiwa dangin Abban su Mubarak ziyara, sannan ta wuce gidan kakar ta Gwaggo kulu wadda tsufa ya ka ma ta sosai, irin kulawa da taimakon da Ammi ke yi mata su ke saka ta k'ara nadamar abubuwan da ta yi mata a shekarun baya.

"Haba Gwaggo kar ki da mu kan ki ni wallahi komai ya wuce a guri na, da ma a rayuwa ta ba na kwana da ko wa a zuciya ta, ko yanzu na so in mayar da ke guri na da zama don kin nuna min kin fison zama nan ne shiyasa na k'yale ki, amma duk da hakan zan sa mu wadda za ta rik'a kulawa dake ina biyan ta".

Nan ta yita sakawa Ammi albarka da jin dad'in abinda take mata.

Fitar su daga gidan basu za me ko ina ba sai gidan su Mama Baraka, da murnar ta ta tarye su ta ma rasa ina za ta saka su kan dad'i.

"Mubarak ashe da gaske za ka kawomin ziyara wataran".

"Haba Mama ta yaya zan manta dake a rayuwa ta, ko yanzu tahowa nayi in gaya maki ki had'a kayan ki nan da kwana biyu za mu wuce sokoto".

"Anya hakan na yuyuwa Mubarak?, ko hakan na gode da kulawar ku gare ni sosai Allah ya saka da khairan".

Rufe bakin ta kenan k'anen ta na shigowa gidan, bayan sun gaisa da su Ammi ne Mubarak ya sako buk'atar tafiya da Baraka.

"Gaskiya a duniya banda ko wa bayan ita, bazan iya bari kuje da ita ba, zan dai yi maku alfarma d'aya in har Allah ya horemin na mota to zansa aka wo maku ita tayi maku kwana biyu".

Je kaga damuwa k'arara a fuskar Mubarak, saboda gaskiya yana jin Mama Baraka tamkar Ammi a ranshi, bazai ta6a manta yadda ta taimaka masu ba abu d'aya yake so yagan ta a tare dasu.

Tamkar walk'iya haka ta fad'o d'akin cikin kissa da kisisina ta fara magana.

"Haba maigida ai ko Annabi so ya gode wa, kabar ta ta bi su mana mu in mun sa mu lokaci sai mu rik'a kai mata ziyara, kuma a yanda na fahimci maganganun su ai Bk tamkar gida ce a gare su nasan za ta samu lokacin ka wo muna ziyara ko Anty?".

Duk da ta fahimci cikin kissa ne take maganar duk da shi k'anen na ta bai fahimci komai ba a maganar matar shi to ita ta fahimci inda ta sa gaba.

Saboda da ma ba son zama da ita take yi ba kawai don bata sa mu fuska ga maigidan bane shiyasa take danne wasu abubuwan.

Bata San ce wa har ga Allah ta fi son tabi su Ammi ba, ba akan komai ba sai don samun kwanciyar hankalin ta kuma tasan ce wa ba za su ta6a wulak'anta ta ba domin sun san darajar ta.
   Kawai bata so ta nuna tana son binsu ne k'anen na ta yaga bata damu dashi ba, ko yaga ce wa don ta ga masu kud'i ne za ta guje su.

"Shikenan ba matsala sai ta shirya kayan ta in za su wuce suje da ita, amma don Allah yaya kar ki guje mu in da ma ta samu ki rik'a kawo mana ziyara".

"Kakka da mu insha Allah duk k'arshen wata zan rik'a kawo ta, kuma za ku rik'a gaisawa a waya", cewar Mubarak.

Akan murnar an bar shi yaje da Mama Baraka dubu goma ya fitar ya bawa k'anen nata.
    Shi ko je kaga murna gurin shi shi da matar shi sai godiya suke zabgawa, da hakan suka wuce kan ce wa in zasu wuce za su zo suje da ita.

****

Gama breakfast d'in su ke da wuya ta zura da gudu sai toilet, amai ne take lezayawa tamkar za ta had'o da hanjin ta.
    Cikin tashin hankali ya mara mata baya ya tallafo ta sai sannu yake zabga mata, wanda da taimakon shi ta wanke bakin ta had'e da fuskar ta.

Suna dawowa falon ta k'ara wani yunk'uri na amai, tallafo ta d'in da zai yi su koma toilet ta ke ta wanke shi tsaf da wani aman, hakan ya kai ta toilet sai da ya yi mata wanka ya gyara ta sannan ya yi wanka ya shirya suka wuce asibiti.

Awon farko da aka yi mata ya nuna ce wa tana d'auke da ciki na sati uku wanda Mus'ab ya shiga farin ciki sosai, tun asibitin ya rink'a kiran y'an uwa yana gaya masu abin farin cikin da ya sa me su.

Sai dai abu d'aya ke damun shi irin yadda amai ke da munta cikin yini d'aya duk ta zabge tamkar wacce ta yi ciwon sati d'aya.

****

Bayan su Mubarak sun d'auki Mama Baraka ne suka doshi hanyar sokoto, da saukar su ne Haj Maryam ta kar6i mama Baraka da hannun biyu har tana furta ce wa a part d'in ta za ta sauka.

"Duk dai abinki da na yi aure zan d'auke Mama ta".

"Je can tuzuru dakai ka yi kwantai za ka wani ce gidan ka za'a zauna, to bara sai ka k'are ruwan idon na ka".

"Amma ko gaskiya Haj kin gama da yaya, in kika ga matar da zai aura sai kin yi mamaki", ce war Mukarrama.

"Ke gafara can aku, gurin surutu ba'a barki ba ya ba, ke ina na ki mijin yake?".

"Ai ko yau d'innan za ki gan shi, don ca nayi yabari sai yaya Mubarak ya dawo sannan yazo gaida shi", tana maganar da murmushi a fuskar ta.

Da hakan ko wa ya wuce part d'in shi, har Umma ta yi murna da zuwan Mama Baraka.

****

*BAYAN SATI BIYU*

Soyayya ta k'ullu tsakanin Mukarrama da Nibras, sai kuma Mubarak da Imtihal d'iyar Haj Maijidda wanda Ammi ta fi ko wa jin dad'in wannan zumuncin da suka k'ulla tsakanin su, sai kuma Iman da Sudais abokin Haydar, fata d'aya Allah ya nuna mana lokaci musha shagali.

****

"Ni fa wannan cikin ya fara da muna kullum cikin ciwo da k'arin ruwa, duba kaga yanda duk ta zabge tamkar wacce ta shekara kwance tana jinya".
   Mus'ab ne ke ta yiwa Dr Shureim mi ta kan drip d'in da za'a sakawa Musirrah.

"Abin fa sai da hak'uri saboda duk mata hakan suke ta wahala wani lokaci sai cikin ya yi k'wari za kaga sun rage laulayin".

"Gaskiya ina ganin Hayatee ta fi ko wa wahala ji fa yanda komai taci sai ta mayar dashi".

"Kai dai na tane kasani shiyasa".

Hakan dai ya saka mata drip d'in yana mai luradda Mus'ab matsalolin da mata ke fuskanta ya yin d'aukar ciki.

(Na gode sosai da kulawar ku a gare ni, na ji sauk'i sosai Allah yabar zumunci)

*SDY JEGAL*

www.sadijegal.blogspos.com

Dedicated to Sanah S. Matazu.
[7:28AM, 10/17/2016] *SDY* *JEGAL*: �� _SANADIN_ _K'UNCI_7⃣3⃣/7⃣4⃣��

*BAYAN WATA TARA*

Yau ne Musirrah ta tashi da nak'uda wanda tun safe take 6oyewa Mus'ab saboda gudun shiga damuwar shi, akan ganin ita ke da cikin amma tamkar ya fi ta shiga damuwa sanadiyyar yadda cikin ke mugun wahalarda ita.
    Tun shigar cikin ta wata takwas Mama Baraka ta ta re gidan su domin ba ta kulawa yadda ya Kama ta.

"Hayatee yau ba za'a yiman rakiya ba ne?".

"K'albee na d'an zazza6i nake ji shiyasa, Allah ya bada sa'a sai ka dawo".

Briefcase d'in hannun shi ya ajiye da saurin shi ya hawo saman bed d'in, hannun shi ya Kai yana ta6a jikin ta ya ji alamar za fi kad'an.

"Ka ta shi ka wuce kasan na gaya ma duk abinda naji ko da kana office ne Zan kira ka, kuma ka ga Mama na kusa ai".

"Yanayin kine bai min ba yau, saboda ba haka na sa ba ganin ki ba".

Cikin k'arfin hali ta sauko daga saman bed d'in ta d'auki briefcase d'in shi, ta sa d'ayan hannun ta ta sagala a kafad'ar shi suka wuce har gurin motar shi.
   Cikin walwala yaja motar shi ya fice, ita ko ta juya zuwa gida inda take addu'ar in ma haihuwa ce Allah ya kawo mata da sauk'i kar tasha wahala tamkar na d'aukar cikin.

Tana kaiwa falo k'afar ta ta rik'e kuma marar ta ta k'ulle, a tsakiyar falon ta zube cikin yarfe hannu da cizon yatsa.

"Mama! Mama!! Mama!!!",  Sai ana ukun ne ta ji yo ta.
   Da saurin ta ta iso falon had'e da tambayar ta me ke faruwa, nan take gaya mata.

"Y'ar nan kinsan kina jin nak'uda har kika bari maigidan ya fita, da safen nan ya shiga gaida ni har yake jaddada min in kula dake ya ga tamkar yanayin ki ya canza, ashe ko da gaskiyar shi".

Nan ta taimaka mata suka wuce d'aki wanda shigar su da minti biyar haihuwa ta zo gadan-gadan.

Cikin zafin ciwo take rok'on Mama Baraka kan ta kira Mus'ab in ma mutuwa za tayi ta mutu hannun shi.
     "Kar ki damu Musirrah da ikon Allah d'akin ki zaki haihu cikin k'oshin lafiya".

Da taimakon Mama Baraka ta yimata addu'ar nak'uda a ruwa ta ba ta sha.
Cikin yaddar ubangiji ta sunkuto y'ar ta, wanda Mama Baraka na jiran uwar tafiya sai ga wata y'ar ta fito da uwar tafiya.

"Alhmdulillah! Alhmdulillah!! Alhmdulillah", sai da Musirrah ta furta hakan har sau uku.

Mama Baraka sai murmushi take yi. Nan ta fara shirya yaran sannan ta taimakawa Musirrah ta kimtsa.

"To bara in Kira su Ammi domin su zo suga kyautar Allah".

"Mama bara in fara kiran shi sannan a kira su Umma".

"Lallai yaran nan ba kuda kunya, ba ma ni zan yi mai albishir ba ke za kiyi da kan ki".

Nan ta yi murmushi ta sunne kai, Mama Baraka ta fita domin kimtsa guri.

"Wayyo baya na", abinda ta furta kenan daga kiran shi ta kashe wayar tana murmushi.

Cikin saurin da tamkar zai ta shi sama da motar ya iso gidan, wanda ko mota bai rufe ba ya fad'a gidan.

Direct d'akin ta ya fad'a, abinda ya ci karo dashi ne ya sa ya yi turus, sai wani tsadadden murmushi take sako mai mai narkar da zuciya.

Da murmushi d'auke a fuskar shi ya ta ka har bakin gadon da take zaune, da d'ai d'aya ya d'auki yaran ya masu addu'a.

"Wai kina nufin wannan kyautar duk ni kad'ai Allah yabawa?". Nan ya d'aga hannu sama ya yi hamdala ga ubangiji.

Waya ya fitar yadinga kiran y'an uwa da abokanen arzik'i yana gaya masu haihuwar.

Mama Baraka ya sa ta kula da yaran ya sunkuci Musirrah sai mota, asibiti ya nufa da ita domin su duba Mai in bata samu wata matsala ba, saboda yana mamakin yanda ta haifi yara biyu da kanta kuma a gida.

Nan suka duba ta aka gaya mai lafiya lau take, sai wasu allurai da suka mata had'e da maganukkan da suka ba ta.

D'auke da ita ya shigo gidan, Ummy, Umma, Haj Maijidda su ya ci karo dasu zaune a falon sun saka yaran a gaba sai murmushi suke yi.

"Yau na ji d'ibar albarka, mai jegon ce ake tallafowa haka tamkar jinjira?" Cewar Haj Maijidda.

"Haj duba yaran da ta haifa ki gani, in tace tayi tafiya za ta ji ci wo ne".

"Sauke ta nace, ke ko kin lafe ajikin shi tamkar wata jinjira", inji Umma.

Cikin jin nauyi Musirrah ke mutsu-mutsu yasauke ta sai k'ara matse ta yake yi.
   Da saurin shi ya wuce bedroom d'in ta da ita, inda su Haj Maijidda suka bishi da ido alamar mamaki, Ummy ko baki ya mutu sai kunya take ji.

Mela da Iman ya tarar a d'akin sun gyara komai tsaf sun kunna turare sai k'amshi d'akin ke yi.

Sum-sum Iman ta ajiye kaskon turaren da take yawo dashi kusurwa-kusurwa ta fice.

"Ohhh ni Mela na ga ta kaina, ina fatar har nak'udar kai ka mata?". Da murmushi d'auke a fuskar ta.

Cikin murmushi ya sauke ta ya wuce zuwa part d'in shi.

"Angaida laila majnun, a hakan kuka wuto su Umma zuwa nan?".

"Bari ke dai Mela, wallahi duk kunya yake saka ni, ko a gaban wa ba ruwan shi, ko yanzu a falo Haj ta ce ya sauke ni tamkar ta k'ara zuga shi ne ya maza ya shige".

"To ai kinji dad'i saboda kina samun kulawa yadda ya kama ta".

Suna maganar ne Haj Maijidda ta shigo ta tasa k'eyar ta sai toilet ta gasa ta sosai had'e da jan kunnen ta kan yadda za ta kula da kan ta.

Ko da suka fito Mukarrama na rik'e da jinjira d'aya tana juyi da ita a tsakiyar falon, wanda Imtihal ke rik'e da d'ayar jinjirar, sai Anty Rukayya dake zaune gefen gado tana murmushi.

"Tunda kun nu na muna ku y'an dangi ne to za mu tattara na mu mubar maku gidan".

"Hakan ya fi kam Haj, daga ce wa an haihu duk ku kwaso jiki ku cika gidan", cewar Umma.

"A'ah Umma kuyi zaman ku falo mu za mu tsaya a nan ba sai an gan mu ba", inji Mukarrama.

"To shikenan muje falon mu da muka iya taryon bak'i, nan suka had'u suka ko ma falon su Imtihal sai murmushi suke yi.

****

*BAYAN SATI D'AYA*

Gida ya cika mak'il da y'an suna tamkar gidan aure, inda yara suka ci suna Fa'ida da Fadila.

Mela, Mukarrama, Iman, Imtihal matar Mubarak, Anty Rukayya da Musirrah ankon wata shadda suka yi mai ruwan purple ta ci aiki sosai har zuwa wuyan hannun su.

Bahijja matar Dr Shureim da Fateema matar uncle Hakeem, sai kuma Mmn Walida, Sophy, Mmn Ansar, Khairat da Mmn Khalil, inda akaci suna cikin walwala da farin ciki.

Sai k'arfe biyar Mus'ab ya had'a masu wata gajeruwar liyafa iya su yara ba da iyaye ba.

Inda suka had'a da Haydar da Mela, Mukarrama da Nibras, Mubarak da Imtihal, Iman da Sudais, Dr Shureim da Bahijja, uncle Hakeem da Fateema sai kuma Anty Rukayya da Sultan, anyi pics da videos saboda tarihi, Jameel ne da Yusrah basu da wo ba har yanzu.

Anyi taro cikin walwala da nishad'i anci ansha sai dai fatar Allah ya raya Fa'ida da Fadila akan tafarkin islama.

*SDY JEGAL*��

www.sadijegal.blogspot.com

Dedicated to Sanah S. Matazu.
[7:28AM, 10/17/2016] *SDY* *JEGAL*: �� _SANADIN_ _K'UNCI_7⃣5⃣/7⃣6⃣��

*BAYAN KWANA ARBA'IN*

Yau ne Musirrah suka yi kwana arba'in da haihuwar twins d'in ta wato F², wanda dama tun jiya Mus'ab ya shaida mata ce wa ta shirya za su fita gaida iyaye da yan'uwa har da abokanen arzik'i.

Yara sunyi 6ul-6ul dasu wanda inka dube su zaka rantse da Allah kowannen su shi kad'ai aka haifeshi.

Bayan sun shirya ne suka fito har Mama Baraka domin ta ce za ta ko ma gidan Ammi tunda sun yi arba'in, in ya so daga baya a sa mo masu y'ar reno.
    Sun had'awa Mama Baraka goma ta arzik'i wanda kan murna har da kukan ta, ita kam tasan lallai wanda Allah bai bawa haihuwa ba yana cikin damuwa, amma ita kam yaran Ammi biyu da Allah ya ba ta sun cire mata duk wata damuwa ta rashin haihuwa.

Da hakan suka fito basu zarce ko ina ba sai gidan su Musirrah. Nan aka yita murnar ganin y'an biyu, ba kamar Umma dake tarairaya da yaran tamkar ta had'iye su saboda kawaicin Ammi ga yaran.

Haj Maryam ma ta yaba da girman yaran har tana tsokanar Musirrah ce wa yaran sun fita girma da kuzari lokacin da tana k'arama.

"Ka jini da mata kamar kinsan k'urciya ta kina wani zuzuta yaran ki sun fini girma".

Karaf Mama Baraka ta kar6e "Ai ko Haj banga abinda yaran ki za su gwada wa y'ata ba, don itama da tana k'arama tubarakallah.

Nan dai su Ammi suka rik'a murmushi. Mama Baraka ta fitar da kayan da su Musirrah suka ba ta ta nunawa su Umma nan suka taya ta godiya had'e da saka masu albarka.

Hakan Umma ta kwashi yaran ta kaiwa Abba su sai washe baki yake yi yana kallon yaran had'e da yi masu wasa.

Suna fita daga gidan suka wuce gidan Anty Rukayya, nan dai suka zazzaga dangi sai marece suka wuce gidan su Mus'ab wanda Ummy ta ma rasa Ina za ta saka yaran kan murna, Baffa ma ya sakama rayuwar yaran albarka sai k'arfe 09:00pm suka wuce gidan su.

A gajiye suka koma gidan inda suka yi wanka suka kwanta, saboda dama sunci abinci gidan su Mus'ab d'in.

****

*WASHE GARI*

Breakfast kawai suka yi suka fice, yau gidan Iman aka fara zuwa nan ya barta ya fice.

Da murnar ta ta tarye su in da take turo d'an cikin ta da bazai wuce wata bakwai ba.

Daga nan sai gidan Mukarrama wanda ta lak'e suka fita tare.

A cewar ta za ta raka ta yawon gaida dangi, daga gidan ta suka wuce gidan yaya Mubarak.

Bayan sun gaisa aka ta6a hira har suna tsokanar Imtihal kan ce wa ita da Iman ba'asan wa zai riga wani haihuwa ba.

Gidan Haj Maijidda suka wuce daga nan wanda ta yi murna sosai da ganin su, har ta had'awa Musirrah maganin Mata na gyaran jiki dangin na sha dana turare saboda ita bata wasa ko kad'an shiyasa ko yaushe take manne a zuciyar maigidan, nan Musirrah tayi ta godiya.

Gidan babbar k'awa Mela ne na k'arshe, inda suka tarar da ita zube a falo da uban cikin ta.
   Dariya suka rink'a tutsurawa wanda ya yi sanadiyyar fitowar yayan su Haydar.

"Yaya barka da yau, ya gidan?".

"Ku bari ku k'arasa iskancin da ya ka wo ku gidan sannan mu gaisa".

Musirrah ta ja bakin ta ta tsuke, Mukarrama kuwa tamkar k'ara zuga ta yake yi.

Da saurin shi ya zabura ya yo kanta, bayan Musirrah ta yi saurin 6oyewa.

"Da ki tsaya ki gani in kin wuce duka a guri na".

"Bross fa igiya uku ke saman kaina, wai ko ka manta ne?".

"Ai na za ta ke talatin aka d'aura maki".

Nan dai su Musirrah suka yi ta dariya ita da Mela, saboda zamantakewar Haydar da Mukarrama na burge su ko yaushe suka had'u sai sun sayar da hali.

Hakan dai suka yi ta hirar su cikin walwala da nishad'i tamkar kar su rabu.

Da marece Mus'ab ya zo d'aukar su har sun hau hanya ya tuna.

"Kinga ya kamata gobe muje gidan Dr Shureim da gidan uncle Hakeem daga can sai mu wuce Bk, ko ya kike gani?".

"Allah na gaji Abban twin's mu bari nan da kwana biyu".

"Ba matsala Allah yakai muna rai".

"Ameen".

Sai da suka biya suka Fara sauke Mukarrama sannan suka wuce gida.

Suna shiga ana magrib, sallah suka fara gabatarwa sannan ta shiga kitchen abinci mafi sauk'i ta girka masu.

Bayan sun ci sun k'oshi ne suka gabatar da sallar isha sannan suka yi wanka suka kwanta.

(Ga wannan kuyi hak'uri dashi 4 breakfast, lolx)

*SDY JEGAL*

www.sadijegal.blogspot.com

Dedicated to Sanah S. Matazu.
[7:28AM, 10/17/2016] *SDY* *JEGAL*: �� _SANADIN_ _K'UNCI_7⃣7⃣/7⃣8⃣��

*BAYAN KWANA BIYU*

Tun safe suke shirye-shiryen tafiyar su Bk d'in saboda za su biya ta Jega gidan su Dr Shureim da Hakeem.

K'arfe tara dai-dai suka hau hanya. Gidan Hakeem suka fara sauka wanda sunyi murna da zuwan su sosai, kuma sun yi musu tarba wacce ta dace yaran su sai murna suke yi da y'an biyu ji suke yi tamkar a bar masu yaran.

"Kwanan nan fa muke batun kai maku ziyara sai ga shi kun riga mu kun kwashe ladar", cewar Hakeem.

"Wallahi za muje Bk ne ziyara shiyasa na ce ya kamata mu zo mu gaisa".

Hannun Musirrah Fateema ta rik'a suka wuce bedroom d'in ta, nan suka rik'a hira tana k'ara gaya mata dabarun zama da miji.

Kiran da suka ji mazan nai masu ne yasa suka fito.
      "Wai yaushe ne gulma za ta k'arewa Mata ne?, duk hira ba'a yin ta sai an shige uwar d'aka", cewar Hakeem.

"To yanzu ba ga shi kuma mun ba ku guri kun sa mu sake wa ba".

Hakan suka had'a masu goma ta arzik'i suna godiya suka wuce.

Gidan Dr Shureim suka je don ma basu dad'e sosai ba Bahijja da Lateefa sun tarye su yadda ya kama ta. Daga nan suka d'auki hanyar Bk.

Duk inda dangi suke an za ga su har gurin Gwaggon Umma sun je wanda tsufa ya kamata sosai.

Basma ce k'anwar Yasmeen ta mak'alewa Musirrah ce wa sai ta bisu ta rik'a rainon twin's.

Nan ta yi magana da Mus'ab kan cewa y'ar k'anen Abba za ta bi su me yace akai?

"Ba matsala tunda dama dole za mu ne mi mai renon su, saboda haka ta had'a kayan ta sai mu wuce da ita".

Da hakan suka wuce ta re da Basma y'ar kimanin shekara goma sha d'aya, sai murna take yi aranta saboda tana son yara sosai.

****

*BAYAN SHEKARA GOMA*

Abubuwa da dama sun faru ciki kuwa harda rasuwar dattijo mai kamala wato Baban Ammi, wanda ta shiga tashin hankali da jimamin rasa shi saboda shi kad'ai yayi mata saura, don kamin rasuwar shi da shekara ukku Gwaggo kulu ta rasu. Sai dai fatar Allah yajik'ansu da rahama.

6angaren su Jameel kuwa ya dawo da nasarori da dama acikin aikin da yaje, yanzu haka yaran shi uku.

****

Fa'ida ce tazo da saurin ta tana fad'in "Mum wallahi ga Fadila can tana dukan Baffa".

Mus'ab ne ya fita ya shiga tsakanin su.

"Haba Baby waya gaya maki ana dukan Baffa na?".

"Abbu shi ne fa yake tsokana ta akan jiya munje islamiya anyi karatu ban iya ba Malam ya dake ni".

"Haba Baffa na ita fa Antyn kace me yasa kake tsokanar ta?".

"Abbu fa kaduba duk girman ta wai bata iya suratul mulk ba, bayan ko gida Mum na koya mana".

"To kasan kowa da K'wak'walwa shi, kuma in kana mata dariya k'ok'arin ka zai koma na ta, kana son hakan?".

"Aah Abbu", da saurin shi ya amsa.

"To karik'a mata addu'a Allah yak'ara mata basira".

Juyawa yayi gurin little Mukarrama dake ta wasan ta da motar yara, cak ya d'auke ta yana duban ta.

"Kina ga su Anty na fad'a baki je kin gaya min ba ko?"

Cikin maganar ta da bata k'ware sosai ba take gaya mai in su Anty na fad'a kan ta ke ciwo.

Da mamaki yake kallon yarinyar saboda miskila ce ta K'arshe sam bata biyo halin mai sunan ta ba.

Haka ya tasa k'eyar yaran duka suka ko ma falo domin yin breakfast.

Shigar su ke da wuya suka tarar Musirrah ta gama jera komai, nan suka hau dinning table domin karyawa.

"Sai Ku shirya za'ayi birthday party na cika 10yrs d'in ku nan da sati d'aya, ana k'arewa sai auren Anty Basma".

Nan suka cukwiy-kuye shi suna murna had'e da furta "Alla ya bar mana kai Abbun mu".

"To ku matsa ku karya shi ku huta", cewar Musirrah.

Cikin sauri suka sake shi sai murmushi suke yi, wanda cikin sauri Baffa ya haura sama domin gaya wa Anty Basma.

****

*BAYAN KWANA BIYU*

Gwaggon Umma ce Allah ya yiwa rasuwa don ma ta yi yawancin rai.

A hanya ne Ammi da Umma zasu je gaisuwa had'e da Mama Baraka ko ince Haj Baraka don Mubarak ya kai ta Makkah, kuma ta yi auren ta da wani abokin Abba shekaru biyar da suka wuce.

Direba ne ya kusa kad'e wata tsohuwa dake jan jiki saman titi ba tada k'afa d'aya.

Umma ce ta fita domin bata hak'uri, had'a idon da suka yi ta zabura da k'arfi saboda ganin Haj karime, duk ta kod'e ta jeme sai warin datti da take yi.

Da sauri ta koma mota had'e da ba direba umurnin yaja suje, hannun da ta rik'a yi masu ne ya sa Ammi ta fita dai-dai matar na kawowa gurin motar.

"Don Allah da son ma'aiki ki gafar ta min Haj Zainab, na ga rayuwa iri-iri nasan hakk'in kune ke bibiya ta".

"Kwatan-kwacin yadda na yi maki nayiwa wata, ashe na ta sharrin ya fi nawa shi ne ta turamin y'an iskan gari suka kwashe komai dana mallaka kuma suka gundulemin k'afa d'aya".

Da ido Ammi ta bi Umma da kallo alamar tambaya.

"Haj Karime ce". Amsar da ta bata a tak'aice kenan.

Wani imani ne ya k'ara ratsa zuciyar Ammi, nan ta k'ara tabbatar da duniya ba bakin komai bace.

"Ki yafe mata Mmn Jameel, ko hakan ta ga jarabawa".

Dak'yar ta furta "Na yafe maki".

Ammi ce da Mama Baraka suka bata kud'i tana ta godiya har da guntun hawayen ta.

Hakan suka ja mota suka wuce, har suka kai suna tad'in rayuwar duniya.

*SDY JEGAL*

www.sadijegal.blogspot.com

Dedicated to Sanah S. Matazu.
[9:14AM, 10/17/2016] *SDY* *JEGAL*: �� _SANADIN_ _K'UNCI_7⃣9⃣/8⃣0⃣��

*BAYAN SATI D'AYA*

Yau ne ake ta shirye-shiryen birthday party na Fa'ida da Fadila murnar cikar su shekara goma.

Babban hall ne suka ka ma domin gudanar da party d'in inda abin ya had'a har da kakannin su.

6angare uku akayi nasu Umma daban, sannan su Mus'ab, sai na yaran.

Anko ne suka yi gwanin sha'awa, su Ammi wani Jan less suka saka Ummy, Umma, Ammi, Haj Maijidda da kuma Mama Baraka.
   Sai kuma Abba, Baffa, Alh Sani da kuma Alh Mu'azzam mijin Mama Baraka da suka saka wata bugaggar farar shadda.

Sai 6angaren su Musirrah da suka saka material kalar lemon green, Anty Rukayya, Musirrah, Iman, Mela, Mukarrama, Imtihal, Yusrah, Bahijja, Fateema, Lateefa sai Basma.
    Su ma Jameel, Mus'ab, Haydar, Nibras, Shureim, Sudais, Sultan da Hakeem suko voil kalar lemon green suka saka.

Sai 6angaren yaran suko kayan kanti ne suka saka, yaran mukarrama uku, na Iman biyu, Mela hud'u, Imtihal hud'u, Yusrah uku, Anty Rukayya biyar, sai su little Lateefa ita da k'annen ta da yaran Fateema.

Hakan suka cika hall d'in mak'il abin gwanin sha'awa, nan aka ci snacks da lemukka sannan su Fadila suka yanka kek.
   Haka suka bi iyayen suna saka masu kek d'in ana tafi raf-raf.

Saida suka k'are da iyayen suka ko ma kan kakannin su, cikin nishad'i suke abin su.

Baffa ne da Abba na k'arshen suna ka wowa gurin su suka yi rad'a nan suka d'ibi kek d'in za su kai bakin su sai suka kauce suka manna masu a hanci.
   Nan yaran suka d'auki shewa da tafi da dariya.

"Yau naji ja'iran yara, me ya hana ku yiwa iyayen ku sai mu da kuka rena?".
Haj Maijidda ce ke bambamin fad'a dasu.

"Granny kishi kike yi an yiwa su Baffa ba'a maki ba". Cewar Adal diyar Mukarrama, tana maganar ne ta nufo su gadan-gadan da cake a hannun ta.

Dak'uwar da Iman ta yi mata ne yasa ta ja birki tana dariya.

Da hakan akayi taro cikin farin ciki, walwala, nishad'i inda families d'in suka zamo abin alfahari.

"Abban twin's wai fa wannan taron duk yaran mu aka yiwa shi". Tana maganar ne had'e da guntuwar k'walla a idon ta.

"Ina tuna irin k'uncin da muka shiga a shekarun baya ni da Ammi da yaya Mubarak".

"Sanadin k'unci ai ya koma sanadin farin ciki, ko ba hakan ba?".

"Tabbas ka zamo linzamin farin ciki a rayuwa ta". Sai da ya faki idon mutane sannan ya saka halshe yana lashe hawayen da ke zubo mata.

*TAMMAT BI HAMDILLAH, INA GODIYA GA ALLAH DA YA NUNA MIN NA KAMMALA WANNAN LABARIN*

*KUSKUREN DA KE CIKI ALLAH YA YAFE MIN*

*DA FATAR ZAKU YI AMFANI DA ABINDA KE CIKI MAI FA'IDA, KU YI WATSI DA AKASIN HAKAN*

Sadaukarwar ta kice Sister Sanah S. Matazu.
Allah yabar k'auna tsakanin mu.

Anty Maijidda Musa ba kina ba zai iya furta godiya zuwa gare ki ba sai dai in kwatanta saboda tsakanina dake sai Allah.

Ku ma ga taku gaisuwar

Anty Ybk
Ummu Abdul
Mmn Haneef
Umma ta Lubiee Mai Tafseer
Zainab (Autar Hjy)
M. Jabonation
Benaxir Omar

Yayye na ga gaisuwar ku.

Anty Innah
Mmn Waleeda
Anty Rukayya
Mmn Meerat
Mmn Abdulmalik
Mmn Ameer.

Three stars
Hindatu Jegal
Nafee Jegal
Aisha Jegal

Five stars
Assy Jegal
Sumee Jegal
Hauwa Jegal
Balkisu Jegal
Asmee Jegal

Yara manyan gobe
Halima
Maryam
Nana Khadija
Abduljalal
Allah ya sakawa rayuwar Ku albarka.

Y'an Uwa na jini
Sis Maryam (Mela)
Sis Atika (Atiks)
Ummu (Mmn Ja'afar)
K'awa ta gari, matsayin ki ba zai ta6a canjawa ba domin kin cancanci hakan.
Shema'u Bello Bari

Ban manta daku ba
Zainab Musa
Lawiza Musa.

K'anne na kaina
Yaha Saddik
Aisha Bizzy
Aisha Yagani
Yasmeeny.

Abokanen karatu na
Aminiya ta Haj Shafa
Saratu (Mrs Abdussalam)
Y'ar gidan Ango.

Naku matsayi na daban ne

Zarah B~B
Hindatu Shehu
Bungud'u
Bebeelo
Zeitunerh Mrs Dr Moh
Mmn Amatullah
Umamat
Mrs Jawaheer
Mumcy na Rabeaht A Danbappah
Mumcy Rabeaht Husain
Mum Faty
Princess Meenat
Blkisu Blymnu
Fati Salihu
Aunty Sis
Aneesa Abubakar Rimi (Anee)
Nana Diso
Deeja Abdul

Kuna raina har kullum

Mmn Shakur
Khairat
Miss Hafcy
Mmn Xeenert
Jamila Moh Ali
Ummietta Wabi
Fatyn Idiriss
Madelty
Ag
Phareederh yahaya
Maryam Yusuf
Ummu Affan
Mrs M. Bawa
Mas'uda (Mmn Walida)
Habiba Yayaji
Ummen Al'amein
Farzana
Maryama
Jidda jangade
Sophy MD
Shatoo Mammaga
Laurat (Mrs Zubair)
Shamseea
Hafsa D
Jidda A.K.A
Innah Habiba
Ameera Maisikeli
Khadija Manga
Mmn Ansar
Mmn Aslam
Nafisa Alu
Maryam G
Mmn Mamee
Ummulkhulthum
Fatima
Mmn Ja'afar
Yaseera

*SDY JEGAL NOVELS*
*M. JABO MUMBARIN NOVELS*
*MUSHA KARATU*
*ZAUREN KARATU*
*ZUMUNCI GROUP*
*GREATEST WOMEN*
*MUM FATY FAN'S*
*ZARAH B~B FAN'S*
*NWA* *KU NA DABAN NE*��

*SDY JEGAL KE GAIDA DUK MASOYAN TA WA'ANDA TA SANI DAMA WA'ANDA BATA SANI BA*

*NA YI K'OK'ARIN SAKA SUNAYEN KU DUKA SAI DAI HAKAN BAI SAMU BA SABODA YAWAN KU, DA FATAR DUK WANDA BAIJI SUNAN SHI BA ZAI YI HAK'URI KUMA YA YIWA Y'AR MUTAN JEGA UXURI*

*NA GAIDA KOWA DA KOWA KYAUTA*��

*SAI KUN JINI A WANI SABON NOVEL NAWA MAI SUNA.........*

*SDY JEGAL*��

www.sadijegal.blogspot.com

Dedicated to Sanah S. Matazu.